Ƙananan Hukumomin Kano 14 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwan Sama — NiMET
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙananan Hukumomin Kano 14 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwan Sama — NiMET

byAbubakar Sulaiman
1 year ago
Ambaliyar Ruwa

Hukumar Kula da Yanayi ta Kasa (NiMET), ta gargadi wasu kananan hukumomi 14 daga cikin 44 na Jihar Kano, cewar za su iya fuskantar iftila’in ambaliyar ruwa a damina mai zuwa.

Wannan sanarwar ta fito ne daga bakin ko’odinetan shiyyar Kano da Jigawa, Dokta Nuradeen Abdullahi, a yayin wani taron masu ruwa da tsaki kan ambaliyar ruwa.

  • Bincike: el-Rufa’i Ya Kamata Majalisa Ta Gayyato Ba Tsoffin Kwamishinoni Ba – Shehu Sani
  • Za A Bude Shafin Karbar Bashin Dalibai A Ranar 24 Ga Mayu

Kananan hukumomin da za su iya fuskantar barazanar sun hada da Rimin Gado, Tofa, Kabo, Madobi, Garum Malam, Bebeji, Rano, Dawakin Kudu, Warawa, Wudil, Sumaila, Ajingi, Kura da Dala.

Sauran kananan hukumomin guda biyar su ne, Karaye, Takai, Bunkure, Dawakin Tofa, da Makoda, sai dai su ana hasashen ambaliyar ba lallai ta girmama kamar ta sauran ba.

Babban abin jan hankali a nan shi hanyoyin da za a bi domin magance barazanar aukuwar ambaliyar ruwa a daminar da ke tafe.

Dakta Abdullahi ya jaddada muhimmancin hada hannu da hukumar bayar da agajin gaggawa ta Jihar Kano (SEMA), domin tabbatar da cewa masu ruwa da tsaki sun shirya tsaf domin dakile barazanar.

“Mata da yara kanana sun fi zama masu rauni a lokacin damina,” in ji Dokta Abdullahi.

Amma ya bukaci mazauna yankunan da ka iya fuskantar ambaliyar ruwan, da su zauna cikin shiri da kuma bin matakan kariya.

Da ta ke bayani dangane da lamarin, kwamishiniyar jin-kai da kawar da talauci ta jihar, Hajiya Amina Abdullahi, ta tabbatar da kokarin gwamnatin jihar na hana aukuwar ambaliyar ruwan.

Ta ce gwamnatin ta kafa wani kwamiti mai karfi, karkashin jagorancin mataimakin gwamnan jihar, wanda aka dora wa alhakin tsaftace magudanan ruwa a dukkanin kananan hukumomin jihar domin dakile hatsarin ambaliyar ruwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Wike Ya Ba Shugaban Ƙasar Sanigal Bassirou Faye Shaidar Zama Ɗan Ƙasa A Abuja

Wike Ya Ba Shugaban Ƙasar Sanigal Bassirou Faye Shaidar Zama Ɗan Ƙasa A Abuja

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version