Ƙungiya Ta Ƙaddamar Da Rabon Tallafi A  Jigawa
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiya Ta Ƙaddamar Da Rabon Tallafi A  Jigawa

byRabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Jigawa

Shugabar kungiyar Bayar Da Tallafi Ga Marasa karfi da Farfado da Ruhin NIjeriya wato (Grassroots Mobilizers for Better Nigeria Initiative) Amb. Dr. Fatima Muhammad Goni, ta kai ziyara gami da kaddamar da raba kayan tallafi a Garin Dutse dake Jihar Jigawa.

Mai Martaba Sarkin Dutse Alhaji Muhammad Hamim Nuhu Sanusi CFR, shi ya karbi bakuncinta a Fadarsa da ke Garu, inda ya nuna farin cikinsa gami da yabo a gare ta da bayyana cewa masarautar da gwamnatin jihar suna sane da irin ayyuka da take gabatarwa.

  • Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
  • Zulum Ya Amince Da Fitar Da Naira Biliyan 1.3 Don Tallafawa Dalibai 997 Na Aikin Kiwon Lafiya 

Makasudin wannan ziyara dai shi ne neman tabarruki da kuma nuna wa Mai Martaba Sarki wasu aikace-aikace da take yi na tallafa wa masu karamin karfi wajen ganin an gudu tare an tsira tare. Inda ta taba wasu muhimman banraori da suka shafi hidimta wa addini lafiya, da sauran fannoni da ya kamata.

Sannan ta sama wa matasa sama dubu 4 aikin yi a fadin Nijeria a dukkan matakai na kasa.

Duka wannan kokari da Ambasadar ke yi na gani ta tallafa wa masu karamin karfi, kudaden duk da take kashewa tana samunsu ne ta hanyar kasuwancinta da kuma sauran hanyoyi na neman halali.

Sannan an gabatar da wasu daga irin kayayyakin da ta raba da suka hada da kayan makarantar almajirai (Uniform) da take dinkawa na tsangaya musanman a yankunan karkara da sauransu, da kuma sauran sabbin tsare-tsaren ayyukan da za ta gabatar nan gaba.

A karshe Ambasada Goni da mika wa Mai Martaba Sarki Mukamin Uban Wannan Kungiya wato (Grand Patron).

Da take magana da wakilin LEADERSHIP Hausa ta ce wannan aikin ma somin tabi a nan Jigawa domin yanzu ma ta fara, za kuma ta ci gaba kamar yadda yi a fadin jihohin Nijeriya baki daya.

Daga ‘yan Majalissar Sarki da suka tarbe ta akwai Mai Girma Galadiman Dutse, Wamban Dutse, Madaki, Dan Kwano, Sa’i, Dan Masani, Barnawa, Sarkin Fada, Magatakarda, da kuma Jakadan Sulhu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Gaskiya Ta Bayyana Game Da Bullar Mata Masu Shan Jini

'Yansanda Sun Gurfanar Da 'Yan Daba 104 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version