Ƴansanda Sun Damƙe Ƴan Fashi Da Masu Garkuwa Da Mutane 873 A Kano
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴansanda Sun Damƙe Ƴan Fashi Da Masu Garkuwa Da Mutane 873 A Kano

byAbubakar Sulaiman
1 year ago
Ƴansanda

Rundunar ‘Yansandan jihar Kano ta kama mutane 873 bisa zargin aikata laifukan fashi da makami, da garkuwa da mutane, da kuma sauran laifuka yayin zanga-zangar da ta gudana. An kama waɗannan mutanan ne a faɗin jihar, kuma an gabatar da su a Shalƙwatar rundunar da ke Kano a yau Litinin.

Kwamishinan ‘Yansanda, Salman Dogo, ya bayyana cewa an kama mutune 600 bisa zargin aikata laifuka daban-daban yayin zanga-zangar a sassa daban-daban na jihar. Bugu da ƙari, an kama mutum 150 saboda karya dokar hana fita, sannan kuma mutum shida an kama su bisa laifin lalata da fasa shaguna a kamfanin Buga takardu na jihar Kano.

  • Direba Ya Bai Wa ‘Yansanda Jakar Maƙudan Kuɗi Da Ya Tsinta A Kano
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceto Mutum 154 Da Kadarorin Naira Miliyan 80 A Watan Yuli

Dogo ya kuma bayyana cewa an kama mutum 76 da ke ɗauke da tutar ƙasar Rasha, ciki har da wani ɗan ƙasar waje, an samu bindigu kirar AK-47 guda biyu da wasu muhimmiyar dukiya a lokacin da ake gudanar da wannan aiki.

Bugu da ƙari, rundunar ta kama mutane biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, da mutane biyar da ake zargin ‘yan fashi da makami ne, da kuma mutane takwas da ake zargin masu satar motoci ne, tare da samun bindiga kirar Beretta.

Kwamishinan Ƴansandan ya sanar da cewa an ceto mutane 13 da aka yi garkuwa da su yayin gudanar da aikin. Duk waɗanda ake zargi za a gurfanar da su a gaban kotu bayan kammala bincike.

Dogo ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da ba da bayanan sirri don taimaka wa a kama masu aikata laifuka, tare da tabbatar da cewa rundunar tana aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin magance barazanar tsaro a jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara
Tsaro

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

October 4, 2025
Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina
Tsaro

Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

September 22, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Samu Gagarumar Nasara A Wasannin Olympics Na Paris

Kasar Sin Ta Samu Gagarumar Nasara A Wasannin Olympics Na Paris

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version