Ɗaliba Ta Maka Makarantarsu A Kotu, Ta Nemi Diyyar Miliyan ₦505 Kan Cin Zarafinta
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliba Ta Maka Makarantarsu A Kotu, Ta Nemi Diyyar Miliyan ₦505 Kan Cin Zarafinta

byAbubakar Sulaiman
1 year ago
Kotu

Wata ɗalibar makarantar ‘Lead British International School’ da ke Gwarimpa a Abuja mai suna Namitra Bwala, ta kai ƙarar makarantarsu tare da neman a biya ta diyyar zunzurutun kuɗi har Naira Miliyan ₦505 sakamakon laifin cin zali da cin zarafin da aka yi mata.

Idan ba a manta ba LEADERSHIP HAUSA ta rawaito yadda lamarin ya afku bayan da wani faifan bidiyo ya watsu a shafukan sada zumunta wanda a bidiyon aka ga yadda wata ɗaliba mai suna Mariam Hassan take cin zalin Namtira Bwala, bidiyon dai ya janyo cece-ku-ce a kafafen sada zumunta, wanda hakan ya sa mutane da kungiyoyi suka yi tir da kuma kiran a yi mata adalci.

  • Ƙungiyar Ƙwadago Ta NLC Na Zanga-zanga Kan Ƙarin Ƙudin Wutar Lantarki A Nijeriya
  • NFF Za Ta Gabatar Da Finidi George A Matsayinl Sabon Kocin Super Eagles A Yau Litinin

Bayan faruwar hakan, mahukuntan makarantar sun fitar da wata sanarwa domin kwantar da hankula wacce take nuna za su yi bincike kan al’amarin.

Daga cikin waɗanda suka sanya baki a maganar har da ma’aikatar harkokin mata da kuma wacce ta aikata laifin wato Maryam inda ta fitar da wani bidiyon na bayar da haƙuri tare da neman afuwa.

Amma da alama wannan bai sanya iyalan Namitra Bwala su yafe ba. Domin kuwa a safiyar yau Litinin ne, Mista Daniel Madu Bwala, wanda yake a madadin mahaifinta ya shigar da makarantar ‘Lead British International School’ ƙara a wata babbar kotu da ke birnin tarayya Abuja bisa zarginsu da yin sakaci da rufa-rufar abinda ya faru.

Kamfanin lauya mai wakiltar Namtira, Deji Adeyanju and Partners, sun bayyana cewa wanda suke wakiltar na son kotun ta tilastawa makarantar biyansu Naira miliyan ₦500m kuɗin diyya da kuma Naira miliyan biyar kuɗin da suka kashe wajen shari’a saboda sakacin makarantar na rashin ɗaukar matakan da ya dace kamar yadda doka ta tanada.

Bayan makarantar ta biya waɗannan miliyoyin kuɗaɗen, iyalan ɗalibar da aka muzanta na son a rubuta wasiƙar bayar da haƙuri gare su wacce dole sai an wallafa ta a manyan jaridu biyu na Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Ƙungiyar Ƙwadago Ta NLC Na Zanga-zanga Kan Ƙarin Ƙudin Wutar Lantarki A Nijeriya

NLC Na Gudanar Da Zanga-zanga A Ofishin KEDCO Na Kano Kan Ƙarin Ƙuɗin Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version