Ɗaliban Jami'ar Bayero 'Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani

byLeadership Hausa
1 year ago
Jami'ar Bayero

Tsofaffin daliban Sashen’ Koyar da Harsunan Nijeriya na Jami’ar Bayero ‘yan shekarar 2015 sun sabunta Dakin Karatu na Sashen tare da gyaran wasu sassa na Sashen a Jami’ar.

A ranar Alhamis 02 ga watan Mayun 2024 aka gudanar da kasaitaccen bikin bude Dakin Karatu na Marigayi Farfesa M.A.Z Sani da tsofaffin daliban Sashen suka sabunta shi bisa jagorancin shugaban daliban na 2015, Alhaji Hassan Baita Ubawaru, wanda ya samu wakilcin Sakataren Kungiyar daliban, Muhammad Bashir Amin.

Sakataren Kungiyar Dalibai 'Yan Ajin 2015, Muhammad Bashir Amin, yayin da yake yi wa Shugaban Jami'ar Bayero bayani yayin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani
Sakataren Kungiyar Dalibai ‘Yan Ajin 2015, Muhammad Bashir Amin, yayin da yake yi wa Shugaban Jami’ar Bayero bayani yayin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani
  • Za Mu Sabonta Dakin Karatu Na Sashen Harsunan Nijeriya Na Jami’ar Bayero — Hassan Baita
  • Jami’ar Bayero Kano Za Ta Karrama Sanata Barau Da Adesina Da Digirin Girmamawa

A nasa jawabin Shugaban Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya na Jami’ar Bayero, Dr. Jibril Shu’aibu Adamu, ya yaba da kokarin daliban ya kuma sanarwa da Shugaban Jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas, irin kokarin da daliban suke yi na tallafawa Sashen, inda ya ce ko a kwanan nan tsofaffin daliban sun bai wa Sashen sababbin injinan nadar bayanan takardu uku tare da gyaran wasu sassa na Sashen.

Shugaban Jami'ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas da Dr. Jibril S. Adamu da Alh. Baita Ubawaru yayin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani
Shugaban Jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas da Dr. Jibril S. Adamu da Alh. Baita Ubawaru yayin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani

A nasa jawabin, Shugaban Jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya yaba da kokarin daliban da irin tallafin da suke bai wa Sashen, ya kuma yi alkawarin ci gaba da tallafawa Sashen daga bangaren shugabancin Jami’ar.

Sagir ya ce, Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya shi ne Sashe daya rak da ya fi kowane Sashen hulda da kasashen waje da suka hada da kasar Sin da Holandiya da Jamus da dai sauransu.

A jawabin shugaban daliban, Alh. Hassan Baita Ubawaru, wanda ya samu wakilcin Sakataren kungiyar daliban, Muhammad Bashir Amin, ya ce, za su ci gaba da tallafawa Sashen ta bangarori da dama, tare da aiki kafada-kafada da juna don ganin an inganta harkokin koyo d koyarwa da bunkasa Harshe da Adabi da Al’adun Hausawa.

Alh. Baita Ubawaru yayin da yake jawabi a wurin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani a Jami'ar Bayero.
Alh. Baita Ubawaru yayin da yake jawabi a wurin bikin bude Dakin Karatu na M.A.Z Sani a Jami’ar Bayero.

A nasa jawabin, Alh. Baita Ubawaru, wanda shi ne mahaifin shugaban daliban na 2015, kuma daya daga cikin wandanda suka tallafawa Shugaban Jami’ar wajen kaddamar da bude Dakin Karatun a yayin bikin, ya bayyana farin cikinsa tare da fatan Dakin Karatun ya zama mai amfanar da daliban Sashen da sauran al’umma baki daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Shawara Ya Kamata Malamai Su Rika Bai Wa ‘Yan Kannywood Ba Zagi Ba – Daushe

Shawara Ya Kamata Malamai Su Rika Bai Wa ‘Yan Kannywood Ba Zagi Ba - Daushe

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version