Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Ceto Ya Bayyana Ɗan Siyasar Da Ke Da Hannu Kan Kama Shi
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Ceto Ya Bayyana Ɗan Siyasar Da Ke Da Hannu Kan Kama Shi

bySharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
1 year ago
Gobir

Jim kaɗan bayan gudanar da Sallar jana’izar marigayi Sarkin Kudun Gatawa, Isa Muhammad Bawa ba tare da gawa ba wanda da ‘yan ta’adda suka yi wa kisan gilla, ɗan sa wanda aka kama su tare ya bayyana ɗan siyasar da ya ba wa ƴan ta’addan kwangilar yin garkuwa da Sarkin.

Ɗan Sarkin, Kabiru Isa wanda ‘yan ta’addan suka saki a daren jiya bayan biyan kudin fansar miliyan 60 da babura biyar ba tare da bayar da gawar basaraken ba, ya bayyana cewar Honarabul Aminu Boza ne ke da hannu wajen garkuwa da basaraken.

  • Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Kashe Ya Kuɓuta Daga Hannun ‘Yan Bindiga
  • Gwamnatin Sokoto Za Ta Sayar da Tireloli 300 Na Shinkafa A Farashi Mai Rahusa

An gudanar da Sallar jana’izar basaraken na Daular Gobir a safiyar yau a Kanwuri da ke Sabon- Birni a inda dubban al’umma suka halarta cike da jimami da bakin cikin kisan gillar da aka yi masa.

A wani bidiyon da aka ɗauke shi kan gadon asibiti na daƙiƙu 30, Kabiru wanda shi ne ke tuka Sarkin a mota yayin da aka kama su ya ce Honarabul Aminu Boza ne ‘yan ta’addan suka ce masu ya bayar da Naira miliyan biyar a kama Sarkin. Ya ce da shi da Sarkin duk sun bayyana masu hakan tare da cewar sun ce a ɗora masa tara.

Honarabul Aminu Boza shi ne Ɗan majalisar da ke wakiltar ƙaramar hukumar Sabon-Birni ta Arewa a majalisa dokokin Jihar Sakkwato a jam’iyyar APC ya kuma yi fice a baya wajen shiga kafafen yaɗa labarai yana suka da caccakar gwamnatin Aminu Waziri Tambuwal da ta gabata kan abin da ya kira kasawarta wajen kawar da matsalolin tsaro a Sabon- Birni da Gabacin Sakkwato baki ɗaya.

Dan majalisar wanda daga baya ya canza sheka daga PDP zuwa APC, ba a taba jin ya shiga kafafen yaɗa labarai ya soki gwamnatin Ahmed Aliyu kan ta’addancin da ‘yan bindigar ke yi ba kamar yadda ya yi a baya ba duk kuwa da ta’azzara da lamarin ya ƙara yi a yanzu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Majalisar Jihar Kebbi Ta Amince Da Ƙudirin Gyaran Dokar Ƙananan Hukumomi

Majalisar Jihar Kebbi Ta Amince Da Ƙudirin Gyaran Dokar Ƙananan Hukumomi

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version