Dan Takarar PDP Na Zamfara, Dauda Lawal Ya Taya Sen. Adeleke Murnar Lashe Zaben Osun
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Takarar PDP Na Zamfara, Dauda Lawal Ya Taya Sen. Adeleke Murnar Lashe Zaben Osun

byBello Hamza
3 years ago
Dauda Lawal

Dan takarar gwamnan jihar Zamfara a karkashin jam’iyyar PDP, Dr. Dauda Lawal ya taya zababben gwamnan jihar Osun, Adeleke Nurudeen Ademola murnar nasarar da ya samu a zaben gwamnan jihar Osun da aka kammala.

Jami’in zaben Gwamnan jihar Osun na Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC, Farfesa Oluwatoyin Ogundipe a safiyar ranar Lahadi, ya bayyana Ademola Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaben. Tsohon Sanatan ya zama wanda ya lashe zaben gwamnan ne da kuri’u 403,371.

  • Kamfanin Aero Ya Dakatar Da Sufurin Jiragensa Kan Tsadar Farashin Mai Da Wahalar Samunsa

Lawal a cikin sakon taya murnar da ofishinsa na yada labarai ya fitar a Gusau, babban birnin jihar Zamfara ya ce yana da yakinin Adeleke zai iya aiwatar da abin da al’ummar jihar Osun ke bukata.

Ya ce nasarar da aka samu wata alama ce da ke nuna cewa al’ummar Jihar Osun da ma Nijeriya baki daya har yanzu suna da kwarin guiwar cewa jam’iyyar PDP za ta iya samar da kyakkyawan shugabanci da kuma yi wa jama’a hidima mai inganci. Ya bayyana Adeleke a matsayin mutumin da ya dace inda ya ce ko shakka babu zai yi kyakkyawan shugabanci idan aka rantsar da shi a ofis.

“Mutanen Osun sun yi zaben da ya dace ta hanyar zaben Sen. Adeleke na PDP. Zan iya tabbatar wa da mutanen Osun cewa PDP da zababben gwamnan suna da duk abin da ya kamata domin share muku hawaye da samar muku da hanyar ribatar dimokuradiyyar da ta kubuce muku.

“Tare da Sen. Adeleke a kan kujerar mulki, ba na shakkar cewa nan ba da jimawa ba jihar za ta samu ci gaba mara misaltuwa ta fuskacin zamantakewa, tattalin arziki da kuma siyasa”, inji shi.

Dan takarar Gwamnan na PDP na Zamfara ya kuma yaba wa Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, kungiyoyin fararen hula, da Jami’an tsaro na ganin cewa zabin da al’umma suka yi ya yi nasara a jihar ta Osun.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Mahaifin Sanata Ndume, Alhaji Buba Ali Ya Rasu

Mahaifin Sanata Ndume, Alhaji Buba Ali Ya Rasu

LABARAI MASU NASABA

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version