12 Ga Yuni: Atiku, Tinubu Da Obi Da Ragowar Wasu Za Su Sanya Furanni A Kabarin Abiola
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

12 Ga Yuni: Atiku, Tinubu Da Obi Da Ragowar Wasu Za Su Sanya Furanni A Kabarin Abiola

byMuhammad
3 years ago
12

‘Yan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar da takwaransa na Jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, a ranar Lahadi, 12 ga watan Yuni, 2022, jam’iyyar LP ta Peter Obi, da wasu fitattun ‘yan Najeriya da masu fafutukar tabbatar da dimokuradiyya za su ajiye furanni don tunawa da wanda ya lashe zaben shugaban kasa da aka soke ranar 12 ga watan Yunin 1993, marigayi Cif MKO Abiola.

Shugaban kwamitin shirya bikin ranar dimokradiyya na ranar 12 ga watan Yuni, Farfesa Anthony Kola ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.

  • Atiku Zai Yi Wa Tinubu Kwab Ɗaya, Don Ba Tsaransa Ba Ne, In Ji PDP
  • Ni Zan Zaɓi Mataimakina Da Kaina – Tinubu

Ya ce, “A taron tunawa da zagayowar ranar dimokaradiyya na ranar 12 ga watan Yuni, wadda fitattun ‘yan uwa masu rajin kare dimokradiyya a Nijeriya suka kira, na sanar da cewa, ranar za ta karbi bakuncin fitattun ‘yan Nijeriya da masu fafutukar tabbatar da dimokuradiyya.

A ranar Lahadi, 12 ga watan Yuni, 2022, a gidan MKO Abiola, wanda ya lashe zaben shugaban kasa na ranar 12 ga watan Yuni, 1993, wanda ya rasu a gidan yari saboda ya ki yin watsi da wa’adin tarihi da ‘yan Nijeriya suka ba shi kyauta.

“Wannan taron mai cike da tarihi wanda za a gudanar a harabar gidan MKO Abiola da ke Legas mai suna Cibiyar Dimokuradiyya ta Nijeriya ta kungiyar 12 ga watan Yuni, an yi shi ne da nufin tabbatar da amincewa da ranar 12 ga watan Yuni a matsayin ranar dimokuradiyyar Nijeriya a hukumance.

“Don haka, ana sa ran taron mai cike da tarihi za a gudanar da addu’o’i da karramawa wasu da tunawa da ‘yan mazan jiya jarumai da jarumta a fannin dimokuradiyyar Nijeriya da kuma shimfida furen karramawa kan kabarin MKO Abiola domin tunawa da shi, da irin sadaukar da rayuwarsa mai daraja wajen kare hakkinsa.

Damar da al’umar Nijeriya suka ba shi a ranar 12 ga watan Yunin 1993 a lokacin haifuwar mulkin dimokaradiyya a Nijeriya.

“Wasu daga cikin jiga-jigan ‘yan Najeriya da aka gayyata don yin jawabai da karramawa a wajen taron mai taken ‘Fatan Zaben 93 da Yuni 12: Darasi don gudanar da sahihin Zabe a 2023’ su ne Farfesa Wole Soyinka, shugaban taron; Sanata Bola Ahmed Tinubu, da Waziri Atiku Abubakar da Peter Obi, Cif Ayo Adebanjo, Janar Alani Akinrinade, Farfesa Pat Utomi, Dr Olisa Agbakoba, Mr Femi Falana, Mr Mike Ozekhome, Dr Oby Ezekwesili, Sanata Shehu Sanni, Cif Dele Momodu da dai sauransu.

“Hakazalika, an yi gayyaci dukkan gwamnoni masu goyon bayan 12 ga watan Yuni da masu ruwa da tsaki domin su yi jawabi tare da nuna godiya a wajen taron tare da gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu a matsayin babban mai masaukin baki.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
2023: An Bukaci Tinubu Ya Dora Kan Irin Salon Mulkin Buhari Kwabo Da Kwabo

2023: An Bukaci Tinubu Ya Dora Kan Irin Salon Mulkin Buhari Kwabo Da Kwabo

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version