LABARAI
Da Alkawarin Boge APC Ta Yaudari ‘Yan Nijeriya A 2015 – Gwamna Dankwambo

Gwaman jihar Gombe Alhaji Ibrahim Dankwambo kuma dan takarar kujerar shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar PDP ya bayyana cewar yaudara ‘yan Nijeriya aka yi kafin zaben 2015 ta hanyar yi masu karya da sunan canjin da a yau ya jefa su a cikin kuncin rayuwa..
Dankwambo ya bayyana hakan ne jiya a garin Ado-Ekiti da ke cikin jihar Ekiti a lokacin da ya gana da wakilai masu zaben dan takarar shugaban kasa a PDP da ke jihar.
Acewar sa kamata ya yi ‘yan Nijeriya su fi yadda suke a karkashin mulkin APC amma sai suka yi gaggawa wajen neman canji a 2015 wadda jam’iyyar ta yi masu alkawari da sunan canji, yana mai karwa da cewa“dole za mu tabbatar da tsaro, farfado da tattalin arziki ba wai kashe shi ba”.
Akan zaben kujerar gwamna da aka gudannar a kwanan baya a jihar ta Ekiti kuwa ya ce, za su kalubalanci zaben a Kotu.
A nashi jawabin gwamnan Jahar Ayodele Fayose ya bayyana cewa ‘ya’yan PDP a jihar za su dauki matsaya a kan wanda za su zaba a lokacin zaben na fidda gwani na jami’yyar.
-
HANTSI17 hours ago
Atiku Barazanar APC
-
LABARAI2 days ago
Takardun Zaben Neja ta Gabas Da Ta Arewa Sun Yi Batar Laya –Hukumar INEC
-
MANYAN LABARAI1 day ago
Goodluck Ya Bayyana Yadda Za A Magance Magudin Zabe
-
MANYAN LABARAI2 days ago
Da Dumi-Duminsa: An Dage Zabe Zuwa Mako Mai Zuwa
-
LABARAI1 day ago
Zan So Mu Yi Abota Da Atiku Bayan Mun Yi Masa Ritaya Daga Siyasa —Tinubu
-
MANYAN LABARAI1 day ago
Dage Zabe: Ka Da Mu Karaya Akwai Fata –Saraki Ga Al’ummar Nijeriya
-
LABARAI2 days ago
Ina Nan A Nijeriya Ban Je ko’ina Ba, Kuma Zan Fita Kada Kuri’a Gobe –Obasanjo
-
BUDADDIYAR WASIKA16 hours ago
Baba Buhari, Mu Na Murna Da Tazarce