Tauraruwa Mai Wutsiya
Magidanci Ya Kashe Kansa Ta Hanyar Fada Wa Jirgin Kasa

‘Yan sanda a Abuja suna kokarin gano wani mutum wanda ya mutu a tashar jirgin kasa da ke Phikwore cikin garin Kubwa ranar Litinin.‘Yan sanda sun dangata lamarin da cewa, mutumin ya kashe kansa ne lokacin da ya yi tsalle ya fada titin jirgin sa’ilin da jirgi ke wuce wa. Jirgin ya yi gunduwa-guduwa da mutumin, inda aka tattara namansa aka ijiye a dakin ijiye gawargaki da ke babban asibitin Kubwa.
Kakakin rundunar ‘yan sanda reshan Kubwa CSP Surajdeen Ayobami ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a ranar Talata, ya bayyana cbewa, an samu takardar wasiyya a aljihun mamacin. Ya kara da cewa, “Mun samu takarda a aljihunsa wanda yake yi wa Nijeriya da kuma ‘yan Nijeriya addu’a, ya kuma roki iyalansa a kan su yafe masa dukkan laifin da ya yi musu. Akwai lambar waya a cikin takardar, amma ‘yan sanda basu samu wayar ba. “Mun ta kiran lambar wayan, amma ba ta shiga ba, mun tabbatar da cewa, za mu iya gane mamacin idan da mun samu lambar wayan da ke cikin takardan.”
-
MANYAN LABARAI1 day ago
Zargin Iyalan Buhari: Atiku Ya Kasa Bayar Da Hujja A Gaban Kotu
-
LABARAI2 days ago
‘Yan Sanda Sun Damke Mutum 2 Da Takardun Zabe A Jihar Kano
-
MANYAN LABARAI2 days ago
APC A Zamfara: Bamu Samu Wani Sako Daga Ministan Shari’a Ba —Hukumar INEC
-
SIYASA2 days ago
Za A Samu Matsala Idan A Ka Yi Kuskuren Sake Zabar Buhari -Alhaji Salisu Munafata
-
MANYAN LABARAI2 days ago
Buhari Zai Yi Wa ‘Yan Kasa Jawabi Yau Da Magriba –Adesina
-
LABARAI19 hours ago
Kwankwaso Ya Yaba Wa Al’ummar Jihar Kano
-
MANYAN LABARAI8 hours ago
Da Dumi-Duminsa: An Dage Zabe Zuwa Mako Mai Zuwa
-
LABARAI1 day ago
Zaben Gobe Zabi Ne Tsakanin Ci Gaba Da Koma-baya – Shugaba Buhari