MANYAN LABARAI
Zargin Badakala: Ba Ku Da Hurumin Bincikar Ganduje –Kotu Ga Majalisar Jihar Kano

A yau Alhamis babbar kotun jihar Kano, ta fitar da hukuncin da yake ce wa majalisar dokokin jihar Kanon ba ta da hurumin gudanar da bincike kan wasu bidiyoyi da ake zargin na gwamnan jihar ne, yana amsar daloli daga hannun dan kwangila ya na zurawa a aljihun babbar riga.
Mai shara’a Ahmad Badamasi ne ya fitar da wannan hukuncin, inda ya bayyana kwamitin mutum bakwai da majalisar ta kafa, da ma majalisar dokokin gaba daya ba su da hurumin gudanar da wani bincike kan zargin badakalar.
Mai shara’ar ya ce maimakon dan jarida Jafar Jafar wanda shine babban editan jaridar shafin intanet mai suna Daily Nigerian, ya fara sakin hoton bidiyon da ya mika su ga hukumar ‘yan sanda ko ta EFCC, ko wata hukumar da take yaki da cin hanci da rashawa, wadanda aikinsu ne gudanar da bincika kan abunda ya shafi cin hanci da rashawan.
Alkalin ya gargadi ‘yan majalisar da su dakata da gudanar da wannan binciken nasu ba tare da yin wata-wata ba, mai shara’ar ya bada misalin hakan a jihohin Kogi da Delta da aka samu badakala makamanciyar wannan, inda kotu ta bayyana majalisar dokokin jihohi basu da hurumin gudanar da binciken badakala a kan gwamnan jiha.
Lauyan majalisar ya ce zai yi magana da wadanda yake karewa don jin ko za su daukaka kara, duk da mun san hukunci mai karfi ne, tunda hukunci ne da ya dogara da dokar kwansitushan din kasa, don haka za su zauna su ga matakin shara’a da ya dace su dauka.
-
MANYAN LABARAI1 day ago
Zargin Iyalan Buhari: Atiku Ya Kasa Bayar Da Hujja A Gaban Kotu
-
LABARAI2 days ago
‘Yan Sanda Sun Damke Mutum 2 Da Takardun Zabe A Jihar Kano
-
MANYAN LABARAI2 days ago
APC A Zamfara: Bamu Samu Wani Sako Daga Ministan Shari’a Ba —Hukumar INEC
-
SIYASA2 days ago
Za A Samu Matsala Idan A Ka Yi Kuskuren Sake Zabar Buhari -Alhaji Salisu Munafata
-
MANYAN LABARAI7 hours ago
Da Dumi-Duminsa: An Dage Zabe Zuwa Mako Mai Zuwa
-
MANYAN LABARAI2 days ago
Buhari Zai Yi Wa ‘Yan Kasa Jawabi Yau Da Magriba –Adesina
-
LABARAI17 hours ago
Kwankwaso Ya Yaba Wa Al’ummar Jihar Kano
-
LABARAI1 day ago
Zaben Gobe Zabi Ne Tsakanin Ci Gaba Da Koma-baya – Shugaba Buhari