Nahiyar Afirka
Ba Zan Ce Komai Ba Kan Sakin Laurent Gbagbo –Ouattara

Shugaban kasar Kodebuwa wato Alassane Ouattara ya ce ba zai ce komai dangane da sakin da hukuncin kotun Hukunta Manyan Laifuffuka ta Duniya ta yi wa tsohon shugaban kasar, Laurent Gbagbo.
Yayin wata hira ta musamman da RFI, shugaba Ouattara ya ce, ba zai ce komai kan wanke Gbagbo daga zargin da ake yi masa ba, amma kuma ya zama wajibi wani ya dauki alhakin kisan da aka yi wa mutane sama da 3,000 da suka mutu sakamakon rikicin siyasar kasar.
Ouattara ya ce, suna ci gaba da gudanar da bincike domin gano wanda ke da hannu wajen tashin hankalin da ya yi sanadiyar hallaka dimbin mutanen.
Dangane da murabus din shugaban Majalisar Dokokin Kasar, Guillame Soro daga mukaminsa kuwa, shugaba Ouattara ya ce, babu matsala a tsakaninsu, sai dai bambancin ra’ayin siyasa.
Rahotanni na cewa, Soro wanda tsohon jagoran ‘yan tawaye ne, na takun-saka da Ouattara kuma akwai yiwuwar tsayawarsa takarar shugaban kasa.
-
MANYAN LABARAI1 day ago
Zargin Iyalan Buhari: Atiku Ya Kasa Bayar Da Hujja A Gaban Kotu
-
LABARAI2 days ago
‘Yan Sanda Sun Damke Mutum 2 Da Takardun Zabe A Jihar Kano
-
MANYAN LABARAI2 days ago
APC A Zamfara: Bamu Samu Wani Sako Daga Ministan Shari’a Ba —Hukumar INEC
-
SIYASA2 days ago
Za A Samu Matsala Idan A Ka Yi Kuskuren Sake Zabar Buhari -Alhaji Salisu Munafata
-
MANYAN LABARAI2 days ago
Buhari Zai Yi Wa ‘Yan Kasa Jawabi Yau Da Magriba –Adesina
-
LABARAI19 hours ago
Kwankwaso Ya Yaba Wa Al’ummar Jihar Kano
-
MANYAN LABARAI8 hours ago
Da Dumi-Duminsa: An Dage Zabe Zuwa Mako Mai Zuwa
-
LABARAI1 day ago
Zaben Gobe Zabi Ne Tsakanin Ci Gaba Da Koma-baya – Shugaba Buhari