LABARAI
Jami’ar Ilorin Ba Za Ta Lamunci Ayyukan Kungiyar Asiri ba –Rijistara

Rijistaran jami’ar Ilorin dake jihar Kwara, Dakta Folaranmi Olowoleni, ta gargadi dalibai cewa sam-sam jami’arsu ba zata lamunci ayyukan ‘ya’yan kungiyar asiri da tahamulli da miyagun kwayoyi a cikin jami’ar ba, Olowoleni ta bayyana hakan ne a daidai lokacin da ake taron maraba da sabbin daliban da suka shigo makarantar.
Ta kara da gargadin daliban da su kiyaye satar amsa a lokutan jarabawa, sannan su dinga shigar mutumci zuwa makaranta, ta shawarci daliban da su kasance masu aiki tukuru, sannan su bi dokokin makarantar sau da kafa, domin ta hakan ne kawai zasu cimma nasara kamar yadda ya dace.
Itama mataimakiyar shugaban jami’ar, Farfesa Sylvia Malomo, ta bukaci dalibai da su kasance masu halaye na gari abun koyi, sannan su kasance masu tsumi da tanadi, su daina yin almubbazaranci da kudadensu, su guji abubuwa marasa kyau, misali caca da sauran nau’in abubuwa irin cacar.
Shugaban harkokin dalibai shima ya shawarci daliban hanyoyin da zasu bi don cin nasara a karatunsu, sai babban limamin masallacin jami’ar shima yayi wa daliban nasiha mai ratsa zuciya, takwaranshi na addinin kirista shi ma yayi wa daliban nasiha kamar dai yadda sauran masu jawabi suka yi.
-
MANYAN LABARAI1 day ago
Zargin Iyalan Buhari: Atiku Ya Kasa Bayar Da Hujja A Gaban Kotu
-
LABARAI2 days ago
‘Yan Sanda Sun Damke Mutum 2 Da Takardun Zabe A Jihar Kano
-
MANYAN LABARAI2 days ago
APC A Zamfara: Bamu Samu Wani Sako Daga Ministan Shari’a Ba —Hukumar INEC
-
SIYASA2 days ago
Za A Samu Matsala Idan A Ka Yi Kuskuren Sake Zabar Buhari -Alhaji Salisu Munafata
-
MANYAN LABARAI2 days ago
Buhari Zai Yi Wa ‘Yan Kasa Jawabi Yau Da Magriba –Adesina
-
LABARAI19 hours ago
Kwankwaso Ya Yaba Wa Al’ummar Jihar Kano
-
MANYAN LABARAI8 hours ago
Da Dumi-Duminsa: An Dage Zabe Zuwa Mako Mai Zuwa
-
LABARAI1 day ago
Zaben Gobe Zabi Ne Tsakanin Ci Gaba Da Koma-baya – Shugaba Buhari