WASANNI
Juventus Za Ta Hakura Da Pogba Domin Siyan Isco Da James

Kungiyar kwallon kafa ta Jubentus ta bayyana cewa ta hakura da neman tsohon dan wasanta, Paul Pogba daga Manchester United inda zata koma neman Isco na Real Madrid da James Rodriguez shima na Real Madrid wanda yake zaman aro a Bayern Munchen.
Kungiyar kwallon kafa ta Juventus tayi alkawarin kashe makudan kudade a kasuwar siyan ‘yan wasa mai zuwa domin kara karfi inda ta shirya komawa domin siyan dan wasa Paul Pogba dan kasar Faransa.
Kamar yadda rahotanni suka bayyana kungiyar kwallon kafa ta Juventus tana shirin kashe makudan kudade wajen siyan manyan ‘yan wasa a kakar wasa mai zuwa kuma Paul Pogba yana daya daga cikin ‘yan wasan da ake ganin kungiyar zata nema.
Isco da Rodriguez dai kwantaraginsu zai kare a kungiyar Real Madrid a kakar wasa mai zuwa kuma kociyan kungiyar, Santiago Solari baya anfani da Isco a wasannin kungiyar akai akai wanda hakan yasa dan wasan yake ganin zai bar kungiyar.
Dan wasa Paul Pogba dai bashi da niyyar barin kungiyar tun bayan da kungiyar ta kori Mourinho wanda daman dashi ne basa shiri kuma har ya dinga ajiyeshi a wasu daga cikin wasannin kungiyar.
Kawo yanzu dai Manchester United bazata yarda ta siyar da dan wasan nata ba wanda ya taimakawa kasar Faransa ta lashe gasar cin kofin duniya wanda aka buga a kasar Rasha a shekarar data gabata.
-
HANTSI1 day ago
Atiku Barazanar APC
-
RAHOTANNI1 day ago
Ba Mu Da Masaniyar Cafke Wani Da Sakamakon Zabe Na Bogi A Abia, Cewar ‘Yan Sanda
-
MANYAN LABARAI2 days ago
Dage Zabe: Ka Da Mu Karaya Akwai Fata –Saraki Ga Al’ummar Nijeriya
-
KASASHEN WAJE12 hours ago
Mayakan Boko Haram 187 Sun Ajje Makamai A Kamaru
-
BUDADDIYAR WASIKA1 day ago
Baba Buhari, Mu Na Murna Da Tazarce
-
LABARAI2 days ago
Dage Zabe: Ba Karamin Mamaki Abun Ya Bani Ba –Atiku
-
LABARAI10 hours ago
Wani Kusa A APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Bauchi
-
MANYAN LABARAI1 day ago
Ko A Dage Zabe Ko Kada A Dage Sai Mun Kayar Da Buhari, In Ji Kera