MANYAN LABARAI
Zabe: ‘Yan Sanda Sun Kara Tsaro A Ofisoshin INEC

Mukaddashin babban Sufeton ‘Yan sanda na kasa, Mohammed Adamu, ya bayar da umurnin a tsaurara tsaro a duk ofisoshin hukumar zabe da ke duk sassan kasar nan.
Kakakin rundunar, Frank Mba, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranar Lahadi.
Ya ce, duk Kwamishinonin ‘Yan sanda na Jihohi 36 da Abuja, an umurce su da su samar da cikakken tsaro a duk ofisoshin hukumar zaben da kuma kayayyakin zabe na hukumar daga cutarwan kowa, kafin, a lokacin da kuma bayan zaben.
Wannan umurnin ya zo ne awanni kadan da hukumar zaben ta kai rahoto ga babban sufeton na gobara biyu da aka yi a ofisoshin hukumar da ke Abiya da Jihar Filato.
Sanarwar ta Mista Mba ta ce, mataimakin babban sufeton ‘yan sanda na kasa na wannan shiyyan an dora masu nauyin dubawa da tabbatar da tsaron a duk yankunan su.
“Babban sufeton ‘yan sanda yana tabbatar wa da ‘yan Nijeriya rundunar ‘Yan sanda a shirye take da ta sauke nauyin aikin da ke kanta na samar da tsaron da ya kamata a babban zaben da ke tafe,” in ji Mista Mba.
-
MANYAN LABARAI1 day ago
Zargin Iyalan Buhari: Atiku Ya Kasa Bayar Da Hujja A Gaban Kotu
-
LABARAI2 days ago
‘Yan Sanda Sun Damke Mutum 2 Da Takardun Zabe A Jihar Kano
-
MANYAN LABARAI2 days ago
APC A Zamfara: Bamu Samu Wani Sako Daga Ministan Shari’a Ba —Hukumar INEC
-
SIYASA2 days ago
Za A Samu Matsala Idan A Ka Yi Kuskuren Sake Zabar Buhari -Alhaji Salisu Munafata
-
MANYAN LABARAI7 hours ago
Da Dumi-Duminsa: An Dage Zabe Zuwa Mako Mai Zuwa
-
MANYAN LABARAI2 days ago
Buhari Zai Yi Wa ‘Yan Kasa Jawabi Yau Da Magriba –Adesina
-
LABARAI17 hours ago
Kwankwaso Ya Yaba Wa Al’ummar Jihar Kano
-
LABARAI1 day ago
Zaben Gobe Zabi Ne Tsakanin Ci Gaba Da Koma-baya – Shugaba Buhari