Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

2020: Kebbi Ta Samu Rahoton Tashin Gobara 173, Mutum Daya Ya Mutu

by Muhammad
February 18, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Gobara
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Umar Faruk,

Hukumar kashe gobara ta jihar Kebbi, a jiya ta sanar da cewa ta samu rahotonnin tashin gobara 173 da ta yi sanadiyar mutuwar mutum daya a shekarar ta 2020.

samndaads

Daraktan hukumar, Alhaji Yahaya Garba Zazzagawa, ya shaida wa manema labarai a Birnin Kebbi cewa gobarar ta faru ne tsakanin watan Janairu zuwa Disamba shekarar da ta gabata.

“Daga watan Janairu zuwa Disamba a shekarar 2020, mun yi samu rahotonnin tashin gobara 173 da ceto rayuwar mutum daya da kuma daya da ya rasa ransa a tashin gobarar.

Sauran sun hada da watan Yuli tashin gobara 19, sai kuma tashin gobara a watan Augusta 7, Satumba an samu tashin gobara 7, sai watan Oktoba shi ma an samu tashin gobara 7, haka kuma watan Nuwamba an samu tashin gobara 16 daga karshe a watan Disamba an samu tashin gobara 24.

Ya ce “Mutum daya ya rasa ransa a watan Disamba, sai kuma an ceto daya da ransa. An samu raguwar adadin tashin gobara da kuma mutuwar mutane da ke aka rubuce a kundin tarihin tashin gobara na hukumar kashe gobara ta jihar kebbi a shekarar 2019, bisa ga shekarun baya.

“Duk da cewa, mun dauki adadin kididikar gobara 173 sama da na shekarar 2019; amma an samu raguwar mutuwa daga 11 a shekara ta 2019 zuwa guda daya a cikin shekara ta 2020, saboda hukumar ta dauki matakin gudanar da yekuwa da kuma wayar da kan jama’a, kan illolin da hadarin tashin gobara a cikin al’umma, in ji shi Daraktan hukumar da kashin gobara na jihar kebbi Alhaji Yahaya Garba Zazzagawa”.

Zazzagawa ya ce don hana ci gaba da samun barkewar gobara a jihar, ya zama wajibi ga mazauna a ko yaushe su yi taka tsan-tsan wajen amfani da kayan lantarki da sauran abubuwa masu saurin kamawa da wuta don kan a tabbatar da cewa an kashe kayan lantarki a duk lokacin da za a barin gida ko bayan an dauke wutar lantarki.

“Sama da kadarori na sama da Naira Miliyan 240 aka yi asara sakamakon tashin gobarar, da kuma Naira Miliyan 450 na kadarorin da aka adana yayin barkewar gobarar,” inji shi.

Har ila yau, Zazzagawa ya umarci masu shan sigari da su tabbatar cewa ko yaushe basu zubar da sigarin ba , musamman a wuraren da ciyawar take don yana zama sanadiyar tashin gobara kai tsaye. Saboda haka sai an kaucewa zubar da sigari mai wuta a wuraren da bai dace ba, don yana da hadarin gaske.

A cewarsa, hukumar kashe gobara na bukatar samar da karin motocin aiki don saurin magance matsalolin gobara a jihar.

Daga karshe Daraktan ya yi kira ga Gwamnatin Jihar da ta wadata sashen da abubuwan da zaya karkakawa hukumar wurin gudanar da ayyukan ta yadda ya kamata don saurin amsa kiraye-kiraye tsahi da barkewar gobara a duk fadin jihar.

SendShareTweetShare
Previous Post

An Tallafa Wa Kananan Masu Kiwon Kaji 100 A Jihar Abia 

Next Post

2023: Kungiyoyi 40 Ke Neman Sanata Yahaya Ya Tsaya Takarar Gwamnan Kebbi

RelatedPosts

Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa

Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Daga Ahmed Muh'd Danasabe, Lokoja Ranar Lahadi da ta gabata...

Yadda Zulum Ya Ziyarci Wadanda Harin Boko Haram Ya Rutsa Da Su A Maiduguri 

Yadda Zulum Ya Ziyarci Wadanda Harin Boko Haram Ya Rutsa Da Su A Maiduguri 

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Daga Muhammad Maitela, Maiduguri Biyo bayan harin da mayakan Boko...

Dalilanmu Na Shirya Aurar Da Zawarawa A Kaduna – Sardaunan Badarawa

Dalilanmu Na Shirya Aurar Da Zawarawa A Kaduna – Sardaunan Badarawa

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Daga Musa Muhammad, Abuja An kammala dukkan shirye-shirye don fara...

Next Post
Kebbi

2023: Kungiyoyi 40 Ke Neman Sanata Yahaya Ya Tsaya Takarar Gwamnan Kebbi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version