Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

2023: APC Na Shirin Cigaba Da Mike Kafa A Mulki

by Muhammad
December 1, 2020
in LABARAI
2 min read
Cigaba
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
  • Jam’iyyar Za Ta Fara Sabbin Rijistar Mambobi 12 Ga Disamba

Daga Khalid Idris Doya

 

samndaads

A wani mataki mai kama da cigaba da mike kafa a mulkin kasar, Jam’iyyar APC da ke mulkin Nijeriya ta shaida cewa, za ta fara sabuwar rijistar mambobi gami da sabunta shaidar zama dan jam’iyya daga ranar Asabar, 12 ga Disamba, 2020, zuwa Asabar 9 ga Janairu, 2021.

Shugaban kwamitin riko na jam’iyyar wanda kuma shi ne Gwamnan Jihar Yobe, Alhaji Mai Mala Buni, shi ne ya shaida hakan a jiya ta cikin sanarwar da ya raba wa ’yan jarida a Abuja, ya na mai cewa, hakan ya biyo bayan shawara da tuntubar masu ruwa da tsaki na jam’iyyar ciki har da Shugaban Kasa Muhamamdu Buhari kan gudanar da aikin yin rijistar.

A cewarsa: “Mun tuntubi masu ruwa da tsaki ciki har da mai girma Shugaban kasa Muhammadu Buhari, fara aikin rijistan sabbin mambobin APC da kuma sabunta katin shaidar zama dan jam’iyya zai gudana a tsakanin ranar Asabar 12 ga watan Disamban 2020 zuwa ranar Asabar 9 ga watan Janairun 2021.

“Kan hakan, kowani mamban jam’iyyarmu ana gayyatarsa da ya sabunta katin zamansa dan jam’iyya a gundumarsa. Har-ila-yau wadanda suke sha’awar kasancewa a cikin jam’iyyarmu mu na gayyatarsu da su yi amfani da wannan damar wajen yin rijista domin shiga ciki jam’iyyarmu.

“Rijistan sabbin mambobin jam’iyya da sabunta shaidar zama dan jam’iyya zai gudana ne a lokaci guda a kowace gunduma da ke fadin kasar nan.”

Ya kuma ce za su tabbatar da kayayyakin gudanar da aikin rijistan sun isa kowace gunduma a kam lokaci, “Aikin rabar da kayan gudanar da ayyukan rijista da sabunta shaidar zama dan jam’iyyar za a raba su ga dukkanin jihohin kasar nan, kananan hukumomi, gundumomi da gundumomi kafin ranar 12 ga Disamban 2020, ranar fara gudanar da rijistan.”

Sai sanarwar ta roki jagororin jam’iyyar a jihohi, kananan hukumomi da gundumomi da su tabbatar da yin duk mai yiyuwa domin tabbatar da aikin sabuntawa da yin rijistan jam’iyyar ya gudana cikin kwanciyar hankali da dadin rai.

Shugaban kwamitin rikon ya sha alwashin cewar za su cigaba da sanar da jama’a halin da ake ciki kan shirye-shiryen yin rijistan domin jama’a su zama suna da cikakken masaniya a kai kamar yadda ya ke bisa doka.

SendShareTweetShare
Previous Post

Ta’addanci: Da Gangan Wasu Kasashe Ke Kawo Wa Nijeriya Cikas Kan Samun Makaman – Lai

Next Post

Kungiyar Ministocin Kasashen OIC Ta Yi Nazarin Hanyoyin Yaki Da Ta’addanci

RelatedPosts

Sheik Karibullah

Sheik Karibullah Ya Nada Alhaji Kabiru Sani Kwangila Khadimul Nabiyya A Taron Maulidin Gidansa

by Sulaiman Ibrahim
24 mins ago
0

A ranar Lahadi ne aka gudanar da Maulidin Manzon Allah...

Magance Matsalar Tsaro

In Dai PDP Na Son Samun Nasara, To Ta Sa Mata A Gaba – Amina Soba

by Sulaiman Ibrahim
29 mins ago
0

Hajiya Amina Adamu Soba, Tsohuwar 'yar takara ce a jam'iyyar...

Allurar Rigakafin Kurona

An Yi Kira Ga ‘Yan Nijeriya Da Su Rungumi Allurar Rigakafin Kurona Da Zarar An Fara

by Sulaiman Ibrahim
34 mins ago
0

An yi kira ga al"umar kasar nan su yi amfani...

Next Post
OIC

Kungiyar Ministocin Kasashen OIC Ta Yi Nazarin Hanyoyin Yaki Da Ta'addanci

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version