2023: Atiku Da Gwamnan Bauchi Sun Sasanta Rikicin Da Ke Tsakaninsu 
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Atiku da Gwamnan Bauchi Sun Sasanta Rikicin Da Ke Tsakaninsu 

bySadiq
3 years ago
Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar, da gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, sun sasanta rikicin da ke tsakaninsu, tare da kudurin yin aiki tare domin samun nasarar zabe a babban zaben badi. 

A baya LEADERSHIP ta rawaito cewa Gwamna Mohammed, ya ce ba zai yi kasa a gwiwa ba wajen ficewa daga kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar PDP na shugaban kasa idan har dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ya gaza fitowa fili ya karyata wadanda ke yi masa aiki tare da bayyana goyon bayansa na sake tsayawa takara a karo na biyu a Jihar Bauchi.

  • 2023: Gwamnan Akwa Ibom Ya Karyata Ajiye Mukaminsa Na Shugaban Yakin Zaben Atiku Da Okowa
  • Yin Amfani Da Yanar Gizo Wajen Raya Duniya

Mohammed, wanda shi ne mataimakin shugaban jam’iyyar a Arewa, ya bayyana haka a wata wasika mai shafi takwas da ya aike wa shugaban jam’iyyar PDP na kasa, Sanata Dr. Iyiocha Ayu.

Ayu da wasu jiga-jigan jam’iyyar sun yi gaggawar kai wa gwamnan Jihar Bauchi ziyara a kwanakin baya.

Duk da cewa taron a sirri aka yi, shugabannin jam’iyyar sun yi watsi da duk wani ra’ayi na sabon rikici a tsakaninsu.

A ci gaba da taron na Bauchi Atiku ya kuma yi wata ganawa da Gwamna Mohammed da wasu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a Abuja a daren ranar Talata.

Da yake bayyana sakamakon taron Abuja da aka yi a safiyar ranar Laraba ta shafinsa na Facebook da aka tabbatar, Atiku ya rubuta cewa: “A daren jiya na karbi bakuncin wasu daga cikin jiga-jigan jam’iyyarmu ta PDP a Abuja, mun tattauna halin da jam’iyyarmu da al’ummar kasar nan ke ciki, kuma muka sake komawa kan lamarin don aikin kishin kasa don murmurewa da dawo da Nijeriya don dawo kasa turbar daidai. – AA.”

Idan dai ba a manta ba PDP ta yi ta fafatawa da kungiyar gwamnoni biyar (PDP G5) wato gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Ezenwo Wike da takwarorinsa na Abia, Oyo, Enugu da Jihar Benue, Okezie Ikpeazu, Seyi Makinde, Ifeanyi Ugwuanyi. da Samuel Ortom.

A baya-bayan nan dai sun kara zafafa adawa da yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Dan Wasan Senegal Mane Ba Zai Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ba Saboda Rauni 

Dan Wasan Senegal Mane Ba Zai Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ba Saboda Rauni 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version