2023: Duk Sanatocin Bauchi Masu Ci Babu Mai Komawa Sun Sha Kaye A Mazabunsu
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Duk Sanatocin Bauchi Masu Ci Babu Mai Komawa Sun Sha Kaye A Mazabunsu

byKhalid Idris Doya
3 years ago
2023

Sanatoci guda uku dukkaninsu ‘ya’yan Jam’iuyar APC ne masu ci a halin yanzu daga jihar Bauchi kuma dukkaninsu babu wanda zai sake komawa Majalisar Dattawa ta kasa daga bayan zaben 2023 domin kuwa sun sha kaye a zaben fitar da gwani da jam’iyyar APC ta gudanar a jihar na Bauchi.

Bayanan da wakilinmu ya tattaro daga jihar ta Bauchi ya nuna cewa Sanatoci guda biyu Lawan Yahaya Gumau (Sanatan Bauchi ta Kudu) da Sanata Adamu Bulkachuwa (Sanatan Bauchi ta Arewa) sun fito neman a sake zabensu a wannan kujerun nasu, inda daliget suka yi waje da su ta hanyar kin zabarsu. Yayin da kuma Sanata Halluru Dauda Jika (Sanatan Bauchi ta tsakiya) ya fito neman tikitin gwamna a jam’iyyar APC wanda kuma ya sha kaye.

  • 2023: Jm’iyyar APC Ta Fara Tantance Masu Neman Takarar Shugabancin Nijeriya

A zaben da aka gudanar na neman tikitin kujerar Sanata a karkashin jam’iyyar APC, wakilinmu ya labarto mana cewa Hon. Sirajo Ibrahim Tanko ne ya samu gagarumar nasarar lashe zaben tikitin Sanatan Bauchi ta Arewa inda ya kada Sanatan da ke ci a halin yanzu Sanata Adamu Bulkachuwa da mummunan rinjaye saboda daliget sunma ki jefa masa kuri’a gaba daya.

Sannan a zaben kujerar Sanatan Bauchi ta Kudu, Hon. Shehu Buba shi ne ya kada Sanatan mai ci, Lawan Yahaya Gumau da kuri’u kalilan.

Sai kuma tikitin Sanatan Bauchi ta tsakiya wanda tsohon shugaban jam’iyyar APC reshen jihar Bauchi, Alhaji Uba Ahmad Nana, ya samu nasarar kada abokan takararsa da suka hada da Sanata Isa Hamma Misau da Hon. Abubakar Shehu.

Kazalika, Sanatan da ke ci a wannan kujerar ta Bauchi ta tsakiya a halin yanzu, Sanata Halliru Dauda Jika, bai fito takarar Sanatan ba domin ya fito an dama da shi ne wajen neman tikitin APC a kujerar gwamnan Jihar Bauchi wanda kuma ya sha kasa a hannun, Air Marshal Sadiq Baba Abubakar.

Tunin Jam’iyyu suka ja daga na neman nasara a kujerun Sanatan musamman jam’iyyar APC da PDP domin dukkaninsu sun yi zaben cikin gida na sanatoci da za su rike musu tuta a zaben 2023.

Da wannan matakin al’umar jihar Bauchi ke sa ran yin sabbin sanatoci daga Jam’iyyun da za su samu nasara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Yan Nijeriya

‘Yan Nijeriya Mu Hankalta, Wasan Kwaikwayo ‘Yan Siyasa Ke Yi Da Mu, In Ji Matasan Arewa A Kudu

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version