2023: Kungiyoyin Mata Da Matasa Sun Bukaci Sanata Jika Ya Koma NNPP Don Yin Takarar Gwamnan Bauchi
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Kungiyoyin Mata Da Matasa Sun Bukaci Sanata Jika Ya Koma NNPP Don Yin Takarar Gwamnan Bauchi

byKhalid Idris Doya
3 years ago
Mata

Wasu kungiyoyin mata da matasa a jihar Bauchi sun yi gangami a ofishin Sanata Halliru Dauda Jika inda suke kiransa da ya sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa jam’iyyar NNPP mai alamar kwando da kayan marmari domin samun zarafin fitowa takarar gwamnan Jihar Bauchi a 2023 da ke tafe.

Wakilinmu ya labarto cewa Sanata Halliru Dauda Jika dai shine ke wakiltar mazabar Bauchi ta tsakiya a Majalisar Dattawa ya fito neman tikitin APC na kujerar gwamna amma Air Marshal Saddique Baba Abubakar ya kayar da shi a zaben fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar a kwanakin baya.

  • Dubban Jama’a Sun Shiga Jam’iyyar NNPP A Neja

Da ya ke jawabi a wajen gangamin, Sadik Abdullahi Kobi, Shugaban kungiyar mata masu dogaro da kansu na jihar Bauchi, ya shaida cewar, babban burinsu shine Sanatan ya amince ya fito neman takarar gwamna a karkashin jam’iyyar NNPP domin cire musu kitse a wuta.

Mata

Ya ce: “Wannan dandanzon mata da matasa da ka gani sun fito ne domin yin kira ga Sanata Halliru Dauda Jika da ya fice daga jam’iyyar APC ya shiga jam’iyyar NNPP domin ya samu damar yin takarar gwamnan Jihar Bauchi a 2023.”

“Daman mun gargadi uwar jam’iyyar APC ta dauki tikitin neman takarar gwamna ta bai wa Sanata Jika saboda shi ne yake tare da mutane, shi ne yake mutunta mutane, shine ya san matsalolinsu, shine yake kawo cigaba ga kuma shine suke so, sabanin wanda aka zo aka kakaba mana da karfin tsiya. Don haka muke son ya bar jam’iyyar ya koma NNPP mu kuma muna tare da shi dari bisa dari.

“Don haka mu a matsayinmu na mata da matasa muna nuna wa Sanata Jika hanyar da ya dace na cewa ya zo ya bi abun da jama’a ke so. Abun da jama’a ke so kuma shine ya shiga NNPP ya mana takarar gwamna.”

Mata

Abdullahi Kobi ya bada tabbacin cewa muddin Jika ya amince ya fito neman takarar gwamna a NNPP tabbas jama’an jihar za su zabeshi domin sun amince da salon jagorancinsa da kyautata musu, “al’umma ke kawo mutum musamman mata. Ka ga kuwa al’ummar ne suka ce lallai ya zo ya musu takara. Don haka muna da kyakkyawar fatan shine zai yi nasara a babban zaben 2023.”

A bangarenta, Malama Saliha Abubakar ta bayyana cewar a shirye suke su shiga lungu da sako domin nema wa Sanata Jika kuri’u, tana mai cewa sun amince da cewa ya fi kowani dan takara dacewar da zai iya jagorantar jihar Bauchi yadda ya kamata.

“Mu iyaye mata mune mu kan irin halin da muke cikin a hali yanzu. Don haka muna rokon ya amsa kiran mu ya koma NNPP domin mu mara masa baya.”

Da ya ke amsar bukatun kungiyoyin a madadin Sanatan, Haruna Muhammad daya daga cikin hadiman Sanata Jika, ya gode wa kungiyoyin bisa nuna damuwa da soyayya ga Sanata Halliru Dauda Jika ya kuma ba su tabbacin cewa za su yi zama na musamman kan wannan bukatar tare da daukan matakin da ya dace domin cigaban jihar Bauchi.

Ya ce, tabbas Sanata Jika na yi ne don al’umma kuma zai sauraro bukatunsu tare da yin abun da dace. Ya ba su tabbacin cewa da izinin Allah Sanata Jika zai yi takarar gwamna a 2023.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Ku Ci Gaba Da Yada Labaran Cin Zarafin Mata Da Kananan Yara —CITAD

Ku Ci Gaba Da Yada Labaran Cin Zarafin Mata Da Kananan Yara —CITAD

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version