Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

2023: Tinubu Ne Ya Fi Cancantar Zama Shugaban Kasa, Inji Wata Kungiya A Bauchi

by
6 months ago
in RAHOTANNI
2 min read
2023: Tinubu Ne Ya Fi Cancantar Zama Shugaban Kasa, Inji Wata Kungiya A Bauchi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Khalid Idris Doya,

Wata kungiya mai suna ‘Disciples of Jagaba ‘Bola Ahmed Tinubu for President 2023’ reshen jihar Bauchi, ta ayyana cikakken goyon bayanta ga jagoran jam’iyyar APC, Ahmed Bola Tinubu da ya zama shugaban Nijeriya a yayin babban zaben 2023.

Kungiyar tana mai cewa, dukkanin wadanda suke ta shinshina kujerar Shugaban kasa bayan saukar Buhari a jam’iyyar APC babu wani da ya kai Tinubu dacewa da cancanta, don haka ne suka ce Bola ne ya kamata ya zama magajin shugaba Buhari.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

A cikin wata sanarwar manema labarai da ko’odintan kungiyar a jihar, Hon. Danjuma Hussaini Sulaiman ya rabar wa ‘yan jarida a Bauchi, ya ce tabbas Tinubu ne yafi cancantar a zaba a matsayin Shugaban kasa a 2023 lura da salon siyasarsa na tafiya da kowa ba tare da nuna banganci ko wariya ba.

Danjuma ya ce, daukar matakin mara wa Bola baya da suka yi, ya biyo bayan irin gogewarsa da kwarewarsa ne da suka duba musamman na zamansa gwamnan Jihar Legas na tsawon shekara takwas da irin cigaba da ya samar.

“Kasancewar Bola Tinubu a matsayin tsohon gwamnan Jihar Legas ya tabbatar da inganta rayuwar al’umma da kuma aiwatar da ayyukan raya jihar. Bisa himmarsa da iya shugabanci nasa, ya tafiyar da gwamnati tare da samar da tagomashi wa kudaden shiga wanda aka samu alfanu sosai.

“Ahmed Bola Tinubu ya kawo cigaba ta kowace fanni a jihar Legas lokacin da ke gwamna. Don haka zaman irinsa a matsayin Shugaban kasa zai kawo cigaba sosai da gyara matsalolin da suke jibge.

“Kari a kan tagomashinsa zai hada kan ‘yan kasa domin baya nuna wariya ko bangaranci. A lokacin da yake gwamna ya baiwa wadanda ba ‘yan asalin jihar Legas ba da dama mukamai a gwamnatinsa. Tabbas irinsa ne suka dace da mulkin Nijeriya.”

Shugaban kungiyar ya kuma kara da cewa, kungiyar ta na da ko’odinetoci a dukkanin kananan hukumomi 20 da suke jihar wadanda suka dukufa yin aiki tukuru domin ganin nasarar Tinubu a 2023.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

LEADERSHIP Ta Lashe Lambar Yabon Jarida Mafi Iya Hulda Da Dillalai

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Harbe Tsohon Dan Takarar Gwamnan Zamfara

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

by Ahmed Muhammad Dan'asabe
15 hours ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

by
17 hours ago
0

...

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

by CMG Hausa
20 hours ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

by
3 days ago
0

...

Next Post
‘Yan Bindiga Sun Harbe Tsohon Dan Takarar Gwamnan Zamfara

'Yan Bindiga Sun Harbe Tsohon Dan Takarar Gwamnan Zamfara

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: