2023: Tinubu Ya Zabi Kabir Ibrahim Masari Daga Katsina A Matsayin Mataimakinsa
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Tinubu Ya Zabi Kabir Ibrahim Masari Daga Katsina A Matsayin Mataimakinsa

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC mai mulki, Asiwaju Bola Tinubu, ya sanar da sunan Alhaji Kabir Ibrahim Masari a matsayin mataimakinsa a zabe mai zuwa na 2023.

byMuhammad
3 years ago
2023

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC mai mulki, Asiwaju Bola Tinubu, ya bayyana sunan Alhaji Kabir Ibrahim Masari a matsayin abokin takararsa a zaben shugaban kasa na 2023.

Daily Trust ta rawaito cewa, Tinubu ya mika sunan Kabir Masari ne a matsayin wanda zai tsaya gabanin wa’adin hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta ba jam’iyyu na su mika sunayen ‘yan takararsu a zaben 2023.

  • 2023: Ban Ce Zan Dauki Mataimaki Musulmi Ba – Tinubu
  • Tun Da Nake Ban Taba Shan Kaye A Zabe Ba – Tinubu

Wasu majiyoyi daga bangaren Tinubu da Masari sun tabbatar wa Daily Trust haka a yammacin ranar Alhamis.

Dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar APC ya fito ne daga kauyen Masari da ke karamar hukumar Kafur a jihar Katsina kuma dan uwan ​​Rt. Hon. Aminu Bello Masari, Gwamnan Katsina.

Mataimaki na dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ya taba zama sakataren jin walwala na kasa a jam’iyya APC a lokacin Kwamared Adams Oshiomhole yana matsayin Jam’iyyar na kasa.

Oshiomhole ya shugabanci APC daga 2018 zuwa 2020.

Abokin takarar Tinubu dan jam’iyyar PDP ne a zamanin marigayi shugaba Umaru Musa Yar’adua.

Bayan rasuwar ‘Yar’aduwa a shekarar 2010, Masari ya koma jam’iyyar (CPC), jam’iyyar da shugaba Muhammadu Buhari ya yi takara a karkashinta amma ya sha kaye a zaben 2011.

Masari ya yi aiki da shugaban kasa Goodluck Jonathan, wanda ya hau mulki bayan rasuwar Yar’adua.

Gabanin zaben 2015, CPC ta ruguje tsarinta zuwa APC, Masari ya koma jam’iyya mai mulki ta APC.

Wasu rahotanni na cewa Tinubu zai maye gurbin Masari kafin zabe saboda yanzu kawai ya mika sunansa ne domin ya cika wa’adin INEC.

“Tinubu yana ci gaba da tuntubar juna kan zabo abokin takararsa. Zai maye gurbin Masari da zarar an zabi wanda ya dace,” inji wata majiya.

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, na jam’iyyar PDP ya bayyana Gwamna Ifeanyi Okowa a matsayin abokin takararsa a zaben 2023,

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Sakon Xi Ya Karfafa Gwiwar Matasan Afrika Wajen Raya Huldar Sin Da Afrika

Sakon Xi Ya Karfafa Gwiwar Matasan Afrika Wajen Raya Huldar Sin Da Afrika

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version