2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna

byYusuf Shuaibu
6 months ago
Siyasa

Yayin da har yanzu ya rage shekaru biyu a gudanar da zaben shugaban kasa a 2027, ‘yan siyasa na ci gaba da gudanar da dubarun siyasa ciki har da tarurruka da kuma ziyarar gidan tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, wanda yanzu ake gani a matsayin sabuwar amarya a fagen siyasar Nijeriya.

Duk da yake gudanar da tarurrukan sun dade suna cikin dubarun siyasar Nijeriya, yanayin da ‘yan siyasa daga jam’iyyar APC mai mulki da ‘yan adawa ke yin safa da marwa zuwa gidan tsohon shugaban kasa a Kaduna don tattaunawar sirri da daukar hotuna tare da shi. Wannan ya faru ne saboda yadda Buhari ya yi watsi da siyasa da kuma karkatar da ‘yan siyasa daga inda suka saba.

  • Manchester Ta Kai Zagayen Semi Final A Europa Bayan Doke Lyon
  • Bai Wa Shanu Guba: Sojoji Sun Shiga Tsakani Domin Dakile Yunkurin Ramuwar Gayya A Filato

Wadannan ziyarar ta kwanan nan ga Buhari, duk da cewa galibi ana alakan ta shi ga neman mulki, wanda ‘yan siyasa suka rike a matsayin wani dubarun neman iko.

Har zuwa yanzu ana ganin Buhari ya rabu da siyasar bayan ya bar ofis, Buhari a hankali ya zama mutum mai tallata ‘yan siyasa, inda bangarori daban-daban suna neman goyon bayansa da albarkarsa. Sauya sheka tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, zuwa jam’iyyar SDP ya kara tsananta jita-jita game da ra’ayin siyasar tsohon shugaban a yanzu.

Don haka, lokacin da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, wanda kwanan nan ya sanar da kwancen hadin gwiwar jam’iyyun adawa don hambarar da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya jagoranci gungun manyan ‘yan siyasa ciki har da El-Rufai da tsohon gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Tambuwal zuwa gidan Buhari a Kaduna, masu sharhi da yawa sun fassara hakan a matsayin wata magana a fili ga tsohon shugaban kasar. An bayyana cewa makusantarsa ‘yan asalin jam’iyyar CPC suna shirin ficewa daga APC.

Duk da cewa Atiku ya dage yayin tattaunawar da ya yi da manema labarai bayan ziyarar cewa ganawar ba ta batun siyasa ba ne, amma jawabin El-Rufai ya nuna karara akwai siyasa a cikin ganawar.

Bayan ziyarar ‘yan adawa kwanaki kadan da na gwamnonin APC, shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya isa gidan Buhari sa’o’i kadan bayan tawagar Atiku, wanda ya kara tsananta siyasa. Ya kuma ba da tabbaci ga ra’ayin cewa shugabannin jam’iyyar APC sun damu da siyasar tsohon shugaban kasar.

Masu lura da al’amura siyasa sun bayyana cewa kalaman da Ganduje ya yi bayan ganawar, ya tabbatar da cewa APC na yin duk mai yiwuwa wajen tabbatar da cewa Buhari ya kasance tare da jam’iyya mai mulki. Wannan matakin na zuwa ne yayin da kawancen ‘yan adawa ke samun karfi, musamman a yayin da ake zaman doya da manja tsakanin gwamnatin Tinubu da ‘yan arewa.

Idan za a iya tunawa a lokacin watan Ramadan, dan shugaban kasa, Seyi Tinubu ya kai ziyarar girmamawa ga Buhari da sauran shugabannin siyasar arewa a lokacin rangadin da ya kai yankin.

Mai sharhi kan harkokin siyasa, Shamsudeen Ibrahim ya bayyana ziyarar da kwamitin gudanarwa na APC da Ganduje ke jagoranta suka kai ga Buhari a matsayin tsoron rasa riko, tsoron rasa arewa, da tsoron rarrabuwar kawuna. Ba ziyarar ‘yan’uwantaka ba ne. Ziyarar neman tsira ne.

Mai sharhi kan harkokin jama’a, Dakta Saidu Dukawa, ya kara da cewa ziyarar ta zama wata manuniya ga jama’a cewa shirye-shiryen zaben 2027.

Dukawa, ya kasance babban malami a jami’ar Bayero da ke Kano (BUK), ya ce, “A bayana, ana yin irin wannan ziyarar ga tsoffin shugabannin kasa da suka hada da Obasanjo da Jonathan don cimma manufofin siyasa, amma yanzu lamarin ya zama tarihi. “

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
An Gudanar Da Bikin Musanyar Al’Adun Al’ummun Sin Da Cambodia A Phnom Penh

An Gudanar Da Bikin Musanyar Al’Adun Al’ummun Sin Da Cambodia A Phnom Penh

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version