Rundunar Sojin Nijeriya ta ce dakarunta sun kashe wasu mayaƙan ISWAP 11 a hare-haren da suka kai Jihohin Borno da Adamawa.
A wata sanarwa da rundunar haɗin gwiwa ta fitar a yau Talata, ta ce lamarin ya faru ne a jiya Litinin bayan da mayaƙan ISWAP suka kai wa sojojin harin kwanton ɓauna a kusa da Garin Giwa, ƙaramar hukumar Kukawa ta Jihar Borno.
- Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
- Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Sanarwar ta ce sojojin sun daƙile harin, inda suka kashe mayaƙa takwas ciki har da kwamandojinsu biyu, tare da ƙwato makamai da babura.
Har ila yau, a Jihar Adamawa, dakarun sojin tare da taimakon mafarauta da ‘yan sa-kai sun kashe wasu mayaƙa uku sannan suka karɓe makamansu.
Sai dai sanarwar ba ta bayyana ko akwai sojojin da suka rasa rayukansu a artabun ba.
Nijeriya dai ta daɗe tana fama da ta’addancin Boko Haram da ISWAP a Arewa Maso Gabas.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp