Kafin Nijeriya ta samu cikakken zaman lafiya da tsaro a fadin Arewa da kuma kudancin kasar, dole ne kowa da kowa ya ba da tasa gudunwara.
Wannan ne ra’ayin mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III da kuma tsohon Shugaban Hafsan Sojoji, Abubakar Danbazau, sun bayyana wannan ra’ayi nasu ne a ranar Litini da ta gabata, a wajen taron koli na dandalin tattaunawa da harkar tsaro, karo na farko da Gwamnatin Jihar Kebbi tare da hadin gwiwar ‘Arewa Broadcast Media Practitioners Forum’ (ABMPF), suka shirya a dakin taro na fadar shugaban kasa da ke Birnin Kebbi.
- Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
- Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe
Sultan Sa’ad, ya bayyana taron a matsayin wanda aka shirya a daidai lokacin da ya dace, kuma ‘yan wannan kasa za su fahimci gaskiya da sanin inda aka sanya gaba, a cewarsa; al’ummar kasar nan na fuskantar hare-hare da kashe-kashe da kuma garkuwa da mutane.
“Wannan wani taro ne da za a tattauna batutuwan da suka shafi rashin tsaro bayan taron da muka gudanar kwanan nan a taron masu rike da sarautun gargajiya da aka yi a Kebbi,” in ji shi.
Ya ce, za su dauki matakin kawar da duk wani nau’in ‘yan fashi da sauran miyagun ayyuka a Arewacin Najeriya.
Haka zalika, ya buga misali da Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, da aka yi garkuwa da shi, kuma aka biya wadanda suka sace shi miliyoyin kudade kafin a sako shi, wanda ya bayyana hakan a matsayin babban abin takaici.
Dangane da batun Shugaban Amurka Donald Trump, Sultan Sa’ad ya bukaci Nijeriya da kada ta bari wasu kasashe su raba kawunansu, ya kuma bayar da tabbacin cewa; duk da kalubalen da ake fuskanta, Nijeriya za ta ci gaba da kasancewa mai girma da kuma ci gaba da samun hadin kai.
Har ila yau, Tsohon Babban Hafsan Sojin Kasa, Abubakar Danbazau, a jawabinsa ya bayar da shawarar cewa; dole ne a magance matsalar rashin tsaro, matsalolin fatara, sauyin yanayi, rashin aikin yi da kuma amfani da kudaden tarayya da aka kayyade.
A cewarsa, kwararar masu tsattsauran ra’ayin addini cikin kasar, ya taimaka wajen tabarbarewar tsaro da ke bukatar daukar matakin yaki da su ko kuma korar su daga kasar baki-daya.
Kazalika, ya kuma bukaci Gwamnonin Arewa da su yi amfani da kudaden asusun tarayya, ta hanyar samar da guraben ayyukan yi da samar da karin masana’antu, domin samun ci gaban tattalin arziki.
A cewar tasa, alkaluma sun nuna cewa; sakamakon ayyukan ‘yan fashi da makami, ya hana kimanin yara miliyan 10 shiga makarantun firamare da sakandare a Arewacin Najeriya.
Gwamnan Jihar Nasarawa, Injiniya Abdullahi Sule, a wani faifan bidiyo da ya gabatar a wurin taron, ya yaba wa wadanda suka shirya taron, musamman ganin cewa; an riga an tattauna batun rashin tsaro a taron Kungiyar Gwamnonin Arewa.
“An yi matukar samun nasarori a wannan taro, kana kuma an tura jami’an tsaro ko’ina a Arewacin kasar nan,” in ji shi.
Gwamna Uzodimma Ya Bukaci Sarakunan Gargajiya Su Jagoranci Yi Wa Kasa Adduo’I’n Zaman Lafiya
Biyo bayan matsin lamba da ake yi wa Nijeriya, kan kashe-kashen da rashin tsaro ke haifarwa, Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jam’iyyar APC, Cif Hope Uzodimma, ya yi kira ga Sarakunan gargajiya da su rika yin addu’o’i, domin samun saukin matsalar tsaro.
Uzodimma, wanda shi ne Gwamnan Jihar Imo, ya jagoranci sauran gwamnonin wajen kai wa Gwamna Mohammed Umar Bago na Jihar Neja ziyara, domin jajanta masa kan asarar rayuka da dama da aka yi a Jihar, a kwanakin baya.
Gwamnan ya kara da cewa, duk da kokarin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, na karfafa tsarin tsaron kasar, ya kamata Sarakunan Gargajiya su yi amfani da nasu hanyoyin da za su kawo karshen rashin tsaro.
“Ina kira ga Sarakunan Gargajiya, da su hada kan al’ummar kasar nan, domin kare al’umma, shugaban kasa, ya himmatu wajen samar da ayyuka, kuma mu a kananan hukumomi; mun dukufa wajen aiwatar da dukkanin manufofinsa, kana kuma; nuna shugabanci na gari shi ne abin da muka sanya gaba,” in ji shi.
Dangane da dalilin ziyarar Gwamna Bago, ya ce; sun je jihar ne, domin jajanta wa gwamnati da jama’a, dangane da haduran jiragen ruwa da na tankar mai da rashin tsaro da suka yi sanadiyyar salwantar rayuka da dama tare da raba mutane da dama da gidajensu.
Ya ce, “Mun zo ne, domin mu yi wa dan’uwanmu ta’aziyya tare da karfafa masa gwiwa, mu kuma bayar da gudunmawar kudi da addu’o’i, da kuma bai wa iyalan wadanda iftila’in ya afka hakuri tare yi musu ta’aziyyar rashin da suka yi”.
“Gwamna Bago, na daya daga cikin mafi kyawun cikinmu, mafi haske, mai kuzari kuma wanda ya san makamar aiki” in ji shi.
Gwamnan Jihar Neja, Bago da Etsu Nupe da Shugaban Masu Rike da Sarautun Gargajiya na Jihar Neja, Alhaji Yahaya Abubakar, duk sun yaba da ziyarar da gwamnonin masu ci suka kawo musu jihar.
Bago ya yi tir da kalubalen tsaro da dimbin bala’o’i da suka addabi jihar, ya kuma ce; gwamnati ta dukufa wajen ganin an samu zaman lafiya.
Gwamnonin da suka ziyarci Minna, sun hada da na Jihohin Delta, Kogi, Ebonyi, Imo da kuma Legas, yayin da Mataimakan Gwamnonin Jihohin Jigawa, Kebbi da Sokoto, suka wakilci nasu gwamnonin.














