ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

by Abubakar Sulaiman
4 hours ago
Zamfara

Shugaban ƙungiyar Fulani makiyaya ta ƙasa (MACBAN), Baba Othman Ngelzarma, ya bayyana cewa Musulmin da suka rasa rayukansu a Zamfara, da Katsina da Sokoto sun ninka adadin Kiristocin da aka kashe a tsakiyar Nijeriya (Middle Belt). Ya yi wannan bayani ne a tattaunawarsa da gidan talabijin ɗin Channels, yana mai ƙalubalantar iƙirarin da ke nuna cewa ana kai wa Kiristoci hari ne musamman a rikice-rikicen da ke faruwa a sassa daban-daban na ƙasar.

Ya ce matsalar tsaro ta rikiɗe zuwa rikici mai cike da rikitarwa da ya ƙunshi bambancin ƙabila, da addini, da rikicin manoma da makiyaya, wanda ya ƙara haifar da ta’addanci, da garkuwa da mutane da kashe-kashe.

  • Kungiyar Fulani Ta MACBAN Ta Nesanta Kanta Daga Zanga-zangar Matasa
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

Ngelzarma ya ce rikice-rikicen ba yanayi ɗaya suke da shi , domin suna bambanta daga wuri zuwa wuri. Ya tunasar da harin 2017 a Sardauna, Taraba, yankin da Kiristoci suka fi yawa, inda sama da makiyaya 700 aka kashe cikin kwanaki biyu, yana mai tambaya kan dalilin da ya sa ba a duba irin wannan adadi da biyu. A Benue kuwa, ya ce tashin hankali ya karu tun daga shekarar 2014 lokacin aiwatar da dokar hana kiwo a fili, wanda ya kara tayar da kura tsakanin manoma da makiyaya a jihar da Kiristoci ke da rinjaye.

ADVERTISEMENT

A jihar Filato, Ngelzarma ya ce rikicin ya fi kama da matsalar ’yan asali da masu shigowa, amma ba rikicin addini kai tsaye ba. Ya zargi gwamnatin jihar ta yanzu da ƙara ruruta wutar rikici a Mangu, yana mai cewa lamarin bai kai haka ba a gwamnatocin baya. Ya bayyana cewa makiyaya sun daɗe suna fuskantar hare-hare a yankin, wanda ya saɓa da labarin da ake yaɗawa cewa sune ke kai hari.

Game da Boko Haram, ya ce kashi 90 cikin 100 na waɗanda suka mutu Musulmai ne, duk da cewa jama’a da dama suna ganin Kiristoci ne ake kai wa farmaki. Ya ce hankalin duniya ya fi karkata kan sace-sacen Chibok ne saboda yankin Kiristoci ne, alhali mafi yawan ɗaliban Dapchi da aka sace Musulmai ne. Ya yi nuni da cewa hakan ya nuna rikicin ya fi rikitarwa fiye da yadda ake yaɗawa.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Ngelzarma ya kuma ce mutanen da suka mutu a Zamfara, da Katsina da Sokoto sun ninka na tsakiya Nijeriya, kuma mafi yawansu Musulmi ne. Ya buƙaci a kalli matsalar tsaron Nijeriya da idon basira da fahimtar bangarori da dama, yana mai cewa idan za a yi hukunci kan rikicin, ya kamata a kira shi da kisa bil’adama gaba ɗaya, ba kisan addini guda ɗaya ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Next Post
Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Kalubalantar Ka’idar "Kasar Sin Daya Tak A Duniya" Tamkar Wasa Da Wuta Ne

LABARAI MASU NASABA

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

November 14, 2025
Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

November 14, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 14, 2025
Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.