• English
  • Business News
Sunday, July 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
3 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon mai ba shugaban kasa Bola Tinubu shawara na musamman kan harkokin siyasa, Dakta Hakeem Baba-Ahmed, ya bayyana cewa babu wani dan takara da zai iya lashe kujerar shugaban kasa a 2027 ba tare da goyon bayan arewa ba.

 

Ya dai bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a Kaduna a karshen mako, Baba-Ahmed, wanda ya kasance tare da tsohon sakataren hukumar inshorar kiwon lafiya ta kasa (NHIS), Farfesa Usman Yusuf, ya jaddada cewa nan ba da dadewa ba arewa za ta ayyana matsayarta na siyasa.

  • ‘Yan Sama Jannati 3 Na Kumbon Shenzhou-20 Na Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniyar Sin Cikin Nasara
  • Idan Kana Son Barin PDP, Yanzu Ne Lokacin – Bukola Saraki

Ya ce, “A cikin watanni shida masu zuwa, arewa za ta yanke shawarar kan matsayarta na siyasa. Idan sauran yankuna suna so su shiga tare da mu, babu matsala kan haka. Idan ba haka ba kuma, sai mu bi hanyarmu ta daban. Abu daya da yake a bayyane shi ne, babu wanda zai iya zama shugaban Nijeriya ba tare da goyon bayan arewa ba.”

 

Labarai Masu Nasaba

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

Ya koka kan halin da kasar ke ciki, kuma ya bukaci ‘yan arewa da su yi taka-tsantsan da ‘yan siyasa masu rarraba kawunan mutane da yaudara, gabanin babban zabe mai zuwa.

 

“Muna son gwamnati da za ta fahimci matsalolinmu kuma ta magance su. Bayan shekaru takwas na mulkin Muhammadu Buhari, mun dauki darasi.

 

”Yanzu haka muna cikin wata gwamnati, kuma har yanzu muna kuka. Kuka kadai ne muka san yadda za mu yi?” Baba-Ahmed ya tambaya.

 

Baba-Ahmed ya ce arewa ta sha wahala sosai a lokacin Boko Haram, wanda ya shafi dukkan kungiyoyi, ciki har da Musulmi da Kiristoci da Fulani da Baju, da sauransu, yana mai jaddada bukatar hadin kai.

 

“Kafin Buhari ya zama shugaban kasa, Boko Haram na kai hari kan masallatai, coci-coci, Abuja da Legas. Wannan shi ne lokacin da ‘yan arewa suka hada kai.”

 

Ya yi gargadi game rashin girmama yankin arewa, yana mai cewa ci gaba da rashin girmama yankin zai haifar da mummunan sakamako.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

Next Post

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

1 day ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

1 day ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

6 days ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

1 week ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 week ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

1 week ago
Next Post
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa

July 19, 2025
An Yi Taron Farko Na Shugabannin Matasa Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka

An Yi Taron Farko Na Shugabannin Matasa Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka

July 19, 2025
Yadda Donal Trump Ya Lashe Zaben Shugabancin Amurka

Putin Ya Fita Daga Raina – Trump

July 19, 2025
Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba

July 19, 2025
Dole Mu Hada Kai Da ‘Yan Siyasa Don Ciyar Da Masana’antar Kannywood Gaba -Shugaban MOPPAN

Dole Mu Hada Kai Da ‘Yan Siyasa Don Ciyar Da Masana’antar Kannywood Gaba -Shugaban MOPPAN

July 19, 2025
Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

July 19, 2025
Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain

Lamine Yamal Na Fuskantar Bincike Kan Bikin Zagayowar Ranar Haihuwarsa A Spain

July 19, 2025
Wakilin Sin: Hukumar Shiga Tsakani Ta Duniya Za Ta Karfafa Warware Takaddamar Kasa Da Kasa Cikin Lumana

Wakilin Sin: Hukumar Shiga Tsakani Ta Duniya Za Ta Karfafa Warware Takaddamar Kasa Da Kasa Cikin Lumana

July 19, 2025
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

July 19, 2025
Xi Da Takwaransa Na Mauritania Ghazouani Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

Xi Da Takwaransa Na Mauritania Ghazouani Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

July 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.