Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Liverpool, Jurgen Klopp, ya bayyana cewa yana da yakinin a hankali kungiyarsa zata koma mataki na daya kamar yadda take a baya idan har suka ci gaba da samun nasara a wasanninsu.
Bayan buga wasanni biyar a jere ba tare da samun nasara ba, kungiyar Liberpool ta huce haushinta a kan kungiyar kwallon kafa ta Tottenham a ranar Alhamis din data gabata in da ta lallasa ta da ci 3-1.
Nasarar da Liverpool ta samu ta hannun ‘yan wasanta Roberto Firmino, Sadio Mane da kuma Aledander Anorld, ta bata damar komawa cikin rukunin kungiyoyi hudu na farko a gasar Premier da maki 37, maki 4 tsakaninta da Manchester City dake kan gaba a halin yanzu.
Yanzu haka dai Manchester United ce ta biyu da maki 40 a gasar ta Premier bayan rashin nasarar da tayi har gida da 2-1 a hannun Sheffeild United a ranar Laraba, Leicester City ce kuma ke biye da Mnachester United din a matsayi na uku da maki 39.
Klopp ya ce idan har ‘yan wasansa suka ci gaba das aka kwazo a wasanninsu na gaba tabbas zasu kai inda suke so kuma ya bayyana cewa watakila kungiyar ta shiga kasuwa domin sayan dan wasan baya wanda zai taimakawa kungiyar.
Bambancin Tuchel Da Pochettino A PSG
Ranar Lahadi kungiyar kwallon kafa ta Monaco ta je har...