A Karo Na 3 Cikin Wata Guda, Jirgin Ruwa Ya Sake Kifewa A Sakkwato
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Karo Na 3 Cikin Wata Guda, Jirgin Ruwa Ya Sake Kifewa A Sakkwato

byAbubakar Sulaiman
1 month ago
Sakkwato

Jihar Sokoto ta sake fuskantar wani mummunan hatsarin jirgin ruwa, karo na uku a cikin wannan watan, inda aka tabbatar da mutuwar mutum biyu yayin da aka ceto mutane tara.

Hatsarin ya faru ne da yammacin Juma’a a kogin Jaranja da ke ƙaramar hukumar Shagari, kamar yadda Shugaban Hukumar Ruwa ta Ƙasa (NIWA) a Sokoto, Bala Bello, ya tabbatar. Ya ce hatsarin ya samo asali ne daga sakaci, da ɗaukar kaya da fasinja fiye da ƙima da kuma karya ƙa’idojin tafiya a ruwa lafiya.

  • BUA Siminti Ya Ƙaddamar Da Shirin Horas Da Matasan Sakkwato
  • Mutane Da Dama Sun Ɓace Yayin Da Jirgin Ruwa Ya Kife A Sakkwato

Kungiyoyin ceto da ta suka haɗa da jami’an NIWA, da hukumar NEMA, da hukumar SEMA ta jiha, da kuma Red Cross sun shiga aikin ceto da bincike domin gano waɗanda ake zargin sun ɓace. Bello ya bayyana cewa suna ci gaba da wayar da kan al’ummomin da ke zaune a bakin ruwa kan muhimmancin amfani da rigar kariya/ceto ta ruwa da kuma bin ƙa’idojin zirga-zirga a ruwa.

A ranar 17 ga Agusta, gwamnatin jihar ta tabbatar da mutuwar fasinjoji huɗu tare da mutane 41 da aka ceto da kuma mutane biyar da suka ɓace a wani hatsarin jirgin ruwa a ƙauyen Kojiyo, ƙaramar hukumar Goronyo. Haka kuma, a ranar 22 ga Agusta, wani hatsari ya auku a ƙauyen Faji na ƙaramar hukumar Sabon Birni. Wannan ya sa hatsarin ranar Juma’a ya zama na uku a cikin wata guda.

Shugaban Sashen Ceto da Farfaɗo da NEMA, Malam Tukur Abubakar, ya tabbatar da cewa ana ci gaba da aikin ceto domin gano fasinjan da ake nema. Wani mazaunin yankin, Malam Abubakar Jabbi daga La, ya ce masu linƙaya sun ceto mutane tara, sun kuma hango gawar mutum ɗaya, yayin da ake ci gaba da neman gawar wata mata da ta nutse.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
NDLEA Ta Kama Wani Matashi Dan Shekara 29 Da Kwayoyin Tramadol 7,000 A Kano

NDLEA Ta Kama Wani Matashi Dan Shekara 29 Da Kwayoyin Tramadol 7,000 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version