Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola

byAisha Seyoji
2 years ago
Mata

Babban abin da ke ba ni haushi da halin mata shi ne, sun mayar da namiji wani BOLA in da za su yada dattinsu.

Ba mutuntawa, sai tsabar korafi da nuna yawan bukatu.

  • Burin Bai Wa Jama’a Shawarwari Ya Sa Na Fara Waka – Jamilu JEY BOY
  • Bayani A Kan Starlink, Da Yadda Tsarinsa Yake

Kudin kunshi, Kudin bleaching, Kudin kitso, Kudin anko, Kudin kati, Kudin Karya, Kudin cefane.

To, Allah Na kallon mu dai mata. Me ya sa na ce haka?

Ba a ce ka da namiji ya yi wa matar shi gata ba. (Haka Allah Ke So) Har lada da farinciki zai samu. Amma yawancin matan yanzu  babu tausayi a zukatansu, sai son kai. Kawai a basu kudi. Wai ba sa ganin kiman namiji sai yana sauke hakkinsu.

Idan bai samu ba, ya zama azzalumi wai…To amma ya samun nashi yake?

Amma ai ana ganin aikin namiji a yanayin matan senatoci, gwamnoni, da sauran masu kudi…yadda mata ke walawa suna kashe kudi.

Sai a ce namiji MUGU ne kawai don ya kasa wasu abubuwan da ake jira ya yi? Ba tausayi? Ba hankurin jira?

Ke mai korafi ba zaki nema ba? Tabbas akwai miyagun maza amma sam ba su da yawa…kururuta YAWANSU ake.

Daga Uwa Aishatu Gidado Idris

IPOH: Yaro Ya Mun Gorin Hausa

Yaro ke nan. Hausa yare daya ne cikin yarukan da nake ji ko nake rubutu da su. In ka ga na yi rubutu da Hausa saboda Hausawa ne (ba yan IPOH) su fahimce ni. Haka kowane marubuci yake yi.

Rubutuna 90% da Turanci nake yi. Ina amfani da Turanci idan Nijeriya nake wa magana. Ina amfani da Hausa idan Arewa kawai na fuskanta. Idan ya kama in ida sako da hillanci sai in yi, mashaallah, don akwai Fulanin da ba su ma san akwai Hausa a duniya ba. Ka yi yawon duniya ka gani. Na fara da Larabci saboda malamai kuma zan habaka shi.

Maganganu irin wadannan za su kawo ma Hausa cibaya ne ba cigaba ba. Alal hakika daba wa kai wuka ne. Idan IPOH Hausa za su yi gori, wadanda za su yi wa gorin suna da yawa. A yau, wadanda ke magana da Hausa sun fi asalin Hausawa yawa. Haka kuma wadanda ke gidajen rediyo, da makarantu kanana da manya, da hukumomin gwamnati inda ake hulda, ko ake yin manufofi (policies) da suke kawo cigaba ga Hausa fiye da kowane harshe. Idan IPOH suka cigaba da gori, anya akwai hikima kuwa?

Akasarin yarukan da suka bunkasa za ka samu wadanda ba yan kabilarsu ba sun taimaka gaya wajen cigabansu. Malaman Larabci da Swahili da Fulatanci za su ba mu misalai da yawa. Hausa ma haka.

Ba zan iya kirga mutanen da ba Hausawa ba da suka taimaka ga daga harshen Hausa, tun daga shi kansa uban gayya Shehu Usumanu Danfodio zuwa manazarta, marubuta, masharhanta, mawaka, malamai, dss, na yau. Kan da za a zayyana maka gudummawar da Fodiyawa suka ba harshen Hausa da za ka sha mamaki. Amma ka kusanci malaman Hausa ka sha labari.

Haka kuma za a cigaba ko yan IPOH ba sa so.

Hattara! Allah ya yi hani da gori. Hausa ni’ima ce gare mu duka. Allah ya ba mu ita ta zame mana zare na dinke Arewa, musulminmu da kiristanmu. Duk lokacin da ka yi magana da Hausa, kana taimaka wa wajen bunkasa Hausa ne. Haka in ka yi rubutu da shi, ko wa’azi, ko magana a gidan rediyo, ko waka, ko wake, dss. Ba gori za a maka ba. Jinjina maka ya kamata a yi.

Duk wadanda suka cigaba, idan suka ji kana harshensu, son ka da girmamaka suke yi. Banda yan IPOH da ke son mai da Hausa baya. Su gori za su maka kamar yanda za ka ji su a comments yanzu nan a kasa.

Mu kam tsakaninmu da Hausa, sai kirari:

Fa Hausa zare ne na dinke mutane Arewa gaba dai fa jigonmu Hausa.

Gyara kawai da zan yi wa yaron shi ne Hausa ba hanyar cin abincina ba ce. Wani ma ya ce sun ba ni kasa na zauna. Nan ma, ba a kasar Hausa nake ba. Hausa harshe ne (Lingua Franca) na yankinmu na Arewa, mallakarmu duka.

Daga Dr. Aliyu U. Tilde

Gajeren Labari Don Nishadi: “Ni Ba’ankare Ne”

Wani mai wasa da kunami duhu ne na tsaka da kewaye a tsakanin mutane a Kasuwa kamar yadda suka saba, sai ya ji a na tsegumin wani makaho da ya zo gittawa yana bara cewa, kar yake da idanunsa. Kawai dai yana kanne su ne don jarabar son yin bara da son banza!.

Ko da ya ji haka, nan da nan sai ya dirfafi wannan makaho yana mai cewa; “Malam Makaho ga sadaka”.

Ko mai karatu kuwa ya san da cewa, wasu manyan kunami uku ya za6o tare da mika su ga wannan Makaho a matsayin sadaka!. Ko da wannan makahon karya ya waigo cikin hanzari, sai dai ya yi kwalli ne da bakaken kunami ne uku duhu. Nan da nan sai ya kada baki ya ce:

“Daga jin muryarka na fahimci kai ba mumini ne ba, saboda haka ba na karbar sadaka a hannun fajiri wanda ba ya ji, ya ki ji, ba ya gani, ya ki gani. Wanda ba ya yarda a zalunce shi ya bar wa Allah”

Sai jama’ar da ke wannan waje suka bushe da  ihu. Su da kansu, sun fahimci Mati Makahon karya tuni ya kai gano cewa an miko masa kunami ne ba sahihiyar sadaka ba. Sai wannan mai wasa da Kunami ya wilkita idanunsa irin na mai yin sigina, kana ya amsawa makahon boge da cewa:

“Haba Malam Makaho, a ina ne aka ce sai a wajen Mumini ne kadai za a amshi sadaka?”.

Makaho; “Ba sai na fada ba, amma dai ai ka san ilmi kogi ne koh. Wai ma tukuna, kai dan wace Mazhaba ne?”.

Mai Kunami; “Ni Ba-malike ne. Kai fa?”.

“Ni Ba’ankare ne, ka ga ma tafiyata, ba na son yawan jidali cikin batun lislama. Ka rike sadakarka, Allah Ya amfana maka caaan”.

Nan da nan Mai Kunami ya yi tamau da cunar rigar makahon karya. Sai jikin Makaho ya hau bari yana mai cewa;

“Bawan Allah, ai ba sai ta kai mu ga wani rikici ba, idan ka gaiyace ni zuwa ga Malikiyyar sai na shiga. Ni dai fatana don Allah ka bar ni na tafi”

Mai Kunami; “Ai ni babban fatana shi ne ka karbi wannan sadaka tawa cikin  ib a sanyi, ba tare da wani yunkurin kafirta  ib a”.

Mai Kunami na magana tare da jefa hannu cikin kwanon da ke dauke da kunami, nan fa Makahon karya yai kukan kura, ya tankwabe hannun mai kunami. Ya saki sandar da ke hannunsa tare da tsallake wani wangalelen kwalbati, ya cika wando nai da iska.

Ganin haka, sai jama’ar da ba su yi masa cikakken sani ba, suka rika yin salallami tare da mamakin ashe Mati ba makahon gaskiya ne ba.

Mukhtar Anwar, ya rubuto daga Kano

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Next Post
An Kashe Fitacciyar Mawaƙiyar Nan Ta Sudan Shaden Gardoodd

An Kashe Fitacciyar Mawaƙiyar Nan Ta Sudan Shaden Gardoodd

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version