Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Abin Jiya Ya Dawo: Mahara Sun Kashe Kwamandan Kare Hadurra, Sun Yi Awon Gaba Da Daya A Zamfara

by Tayo Adelaja
September 24, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Yarjejeniyar Daina Kisa Mu Ka Cimma Ba Ta Garkuwa Ba, In Ji Su

Daga Hussaini Baba, Gusau

samndaads

Abin jiya ya dawo jihar Zamfara, inda a ranar Alhamis da misalin karfe tara na safe ne gungun mahara su ka kai hari ofishin Hukumar Kare Hadura ta Kasa da ke karamar hukumar Tsafe cikin jihar Zamfara su ka harbi rot kwamanda mai suna Mubarak Hamza, wanda nan take ya ce ga garin ku nan, kuma su kai awon gaba da abokin aikinsa mai suna Muhammad Muhammad Birnin Kudu su ka shiga daji da shi.

Bugu da kari, maharan sun shaida wa dangin wasu matan Fulani da a ka kama cewa, ba a yi yarjejeniyar daina kama mutane tsakaninsu da jami’ai ba, illa dai ancimma matsaya a kan cewa, za su daina kashe mutanen da su ka kama ne kurum. To, amma har yanzu ba a tabbatar da dalilin da ya sa a wannan karon su ka bindige jami’in tsaron ba.

Aminu Abubakar Yashi ya bayyana ma wakilin mu cewa, sun tambaye su cewa ba an yi sulhu da su ba? sai maharan su ka ce mu su sulhun kisa ne a ka yi da su ba na sata ba. Donn haka sun dai na kisa, sai idan tsautsayi ya gita.

Jami’n hulda da jama’a na Hukumar Kare Hadora ta jihar Zamfara, Nasiru Ahmad, ya tabbatar da faruwar wannan abu kuma ya shaidama manema labarai cewa, “Hukumar da rundunar ’yan sanda na kokarin gano jami’insu da a ka yi awon gaba da shi.”

Idan ba a manta ba, a makon da ya gabata ne rundunar ’yan sandan jihar karkashin jagorancin Kwamishinan Shaba Alkali ta samu nasarar kwato jami’anta uku da maharan su ka yi awon gaba da su a Keta da ke karamar hukumar Tsafe cikin koshin lafiya.

Haka kazalika ma al’ummar Zamfara ba su manta da wani sabon salon da su maharani su ka fito da shi ba na satar mutane da yin garkuwa da su, sai su ka sace Sarki Maidaraja ta Biyu a jihar, watau Sarkin  Bukuyum, wanda su ka iske shi har fadarsa kuma su kai awon gaba da shi.

Shi ma mataimakin shugaban karamar hukumar Anka masu Ggarkuwar sun yi awon gaba da shi har sai da ya yi kwana da kwanaki, sannan su ka dawo da shi bayan sun ja milyoin Nairori.

Wasu kansilolin har da manyan mutane ma ba su bar su ba da ’yan Kasuwa sama da mutum 40 da su ka yi garkuwa da su duk a cikin wannan shekarar.

Salon satar ya sa masu garkuwa da mutanen su ke  bukatar milyoyin Nairori kafin sun fito da mutanen da su ka sata. Kuma ya sa dole ’yan majalisun jihar da kwamishinoni da masu mukaman siyasa su ka kaurace ma kauyukansu da gonakinsu, don gudun fadawa tarkon masu garkuwa da jama’a a watannin baya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Bambanci Tsakanin Asibitocin Tarayya Da Na Jihohi: Gwamnatin Sakkwato Ta Sami Mafita

Next Post

Yadda Al’ummar Mahaifar Kwamishinan Ruwa Na Gombe Ke Shan Ruwan Kududdufi

RelatedPosts

Garban

Garban Kauye Farawa Ne Allurar Dinke Barakar Kumbotso – Muslihu Yusuf Ali

by Muhammad
17 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana zaben Sabon shugaban Karamar...

Harkokin Noma

Sarkin Noma Ya Shawarci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Kokari Wajen Gyara Harkokin Noma

by Muhammad
18 hours ago
0

Daga Bala Kukkuru, Sarkin Noman Jihar Kano, Alhaji Yusuf Umar...

Kwazon Tambuwal

Hobbasar Kwazon Tambuwal Na Fara Biyan Albashi Daga Haraji A 2023

by Muhammad
2 days ago
0

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar, Gwamnatin Jihar Sakkwato a karkashin jagorancin...

Next Post

Yadda Al’ummar Mahaifar Kwamishinan Ruwa Na Gombe Ke Shan Ruwan Kududdufi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version