Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Abin Kunya A Kaduna: Malamai 21,780 Suka Faɗi Jarabawar ‘Yan Firamare

by Tayo Adelaja
October 11, 2017
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Idris Aliyu Daudawa

Gwamnatin Jihar Kaduna ta shirya wata jarabawa wacce malaman makarantun Firamare 21,780  daga cikin 33,000 suka faɗi. Ita dai wannan jarabawar da suka rubuta, irin wacce ake yi wa ’yan aji huɗu na Firamare ne.

An bayyana maƙasudin jarabawar a matsayin wata hanya ta son gane kaifin hazaƙa da fahimtar da malaman makarantun Firamaren Jihar Kaduna.

Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasiru El-rufai ne ya bayyana hakan a shekaran jiya, yayin da ya amshi baƙoncin wasu jami’an Bankin duniya (IMF), a ziyarar da suka kai zuwa jihar.

Hakanan da akwai matsalar Malami da ɗalibi  a makarantun ƙauye saboda wasu makarantu ana samun yawan malaman bai dace ace suna wurin ba. A wasu Ƙananan Hukumomin ana samun Malamai 1 na kula da ɗalibai 9, wasu kuma Malami 1 shi ke kulawa da ɗalibai100.

Ya cigba da cewar a wani matakin da aka ɗauka na maido da martabar ilmi Darektocin makarantu, sun yanke shawarar sa ‘ya’yansu a makarantun gwamnati, wannan kuma za a fara ne daga shekarar karatun da ake ciki.

Shi ma da yake jawabi mai wakiltar Bankin duniya kuma shugaban tawagar Kunle Adekola, ya nuna jin daɗinsa, akan yadda jihar Kaduna ta maida hankalinta wajen kawo gyara a harkar ilmi, ba musamman ilmi’ya’ya mata, ya ƙara da jaddada cewar jihar ta nuna shirin basu haɗin kai, domin su cimma burinsu.

Ya ce, Bankin duniya ya bada tallafi na Naira milyan 30 a makarantar Firamare ta Rigasa, wadda take da ɗalibai 22,000, a matsayin gudunmawar da ta ba jihar.

Sashen bada tallafi a ɓangaren ilmi na Bankin duniya da sauran wasu mataimaka domin kawo ci gaba, tana bada taimako ne yanzu a jihohin Arewa waɗanda suka kai kusan 13, da kuma jiha ɗaya daga kowane sashe daga cikin sassa shida da ake da su a Nijeriya.

SendShareTweetShare
Previous Post

SHAFIN FARKO

Next Post

An Yi Wa Ɗan Shekaru 70 Rajamu Har Lahira A Kano

RelatedPosts

Hijira

Zulum Ya Bankado ’Yan Hijira 650 Na Bogi

by Muhammad
14 hours ago
0

Ya Sake Koma Wa Dikwa Bayan Harin Boko Haram Daga...

Allurar Rigakafin

An Fara Yin Allurar Riga-kafin Korona a Nijeriya

by Muhammad
3 days ago
0

Yau Ake Sa Ran Buhari Da Osinbajo Za Su Karbi...

'Yan Adaidaita

An Sasanta Yajin Aikin ’Yan Adaidaita Bayan… Motocin ‘Kano Line’  Sun Koma Jigilar Jakara-Kasuwa

by Muhammad
2 weeks ago
0

Babu Hanunmu A Ciki Wannan Yaji – Shugaban ’Yan Adaidaita...

Next Post

An Yi Wa Ɗan Shekaru 70 Rajamu Har Lahira A Kano

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version