Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

‘Abinda Ya Sa Mu Ka Bar Kasuwar Dabbobi Ta Soja Mu Ka Bude Ta Anagada A Abuja’

by Muhammad
February 7, 2021
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Bello Hamza,

Masu sana’ar sayar da dabbobi a tsohuwar karar dabbobi da sojan kasa na Nijeriya su ka samar masu a yankin Giri Abuja, sun yi karin haske a kan lalacewar alakar wadda a ka kulla kamar shekara biyu baya. Jagoran ’yan kasuwar Malam Abdulkadir Muhammad ya ce a sakamakon haka, a yanzu sun yi hijira zuwa wata sabuwar kasuwar kara da su ka kafa a kauyen Anagada da ke kan hanyar Zuba zuwa Gwagwalada a yankin birnin na trayya.

samndaads

Ya danganta matsalar lalacewar alakar kan dalilin rashin hadin kai irin na al’ummar Hausa/Fulani kamar yadda ya yi bayani, lamarin da ya ce ya kai ga wanda ya jagorancesu wajen kullata, ya janye hannunsa alamarin. “Hakan ta sa jagororin soja su ka bukaci da mu bar wajen. “Bayan nan sai a ka tura mana ma’aikata su ka tada mu daga tsohon wajen cikin halin ba-zata da hakan ya jawo mana matsalar rasa yawancin tsoffin abokan huldarmu da ke zuwa daga jihohin arewa da kuma kudu, don huldar kasuwanci.

Malam Abdulkadir ya ce, daga bisani, sun samu Mai-Garin Anagada da Sarkin Fawan wajen, su ka bayyana masu kudurinsu. Ya ce a yanzu sun samu cigaba fiye da na baya tun lokacin da su ka dawo zuwa sabuwar kasuwar karar, wadda ya ci ke ci a kullum, a maimakon bayan kwana hudu irin na lokacin baya. “A saboda haka, mu na kira ga sauran al’ummarmu ’yan kasuwa da su zo mu hada kai mu raya wajen. “Akwai tanadin waje ga sauran ’yan kasuwa masu sayar da kayan abinci irin hatsi da doya da tumatur, kuma mu na kira a garesu da su zo, mu hada kanmu baki daya.

Ya ce mahauta daga kwaryar birni na zuwa kasuwar su na sayan raguna ko awaki ko shanu tare da aikin fida a wajen, kafin wucewa da naman zuwa cikin gari. “Haka kuma mu na samun sakon sautun dabbobi daga abokan huldarmu daga yankuna irin Legas da Fatakwal da sauran wurare na kudancin Nijeriya, a yayin da a wani zubin kuma su ke zuwa nan da kansu don sayan dabbobin, inji shi. Jagoran ya ce akwai shirin kafa katanga da kuma gina shaguna, da ya ce karamar hukumar ta Gwagwalada ke shirin yi masu.

SendShareTweetShare
Previous Post

Wani  Basarake A Yankin Funtuwa Ya Bukaci Al’ummarsa Su Kara Kaimi

Next Post

Korona: An Samu Cinkoson Ababen Hawa A Kano Sakamakon Dokar Takunkumin Fuska

RelatedPosts

Sarkin Musulmi

Fulani Ba ‘Yan Ta’adda Ba Ne –Sarkin Musulmi

by Muhammad
11 hours ago
0

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammadu Sa’ad Abubakar III, ya ce...

Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu

Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu

by Sulaiman Ibrahim
16 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Gusau A shirin Gwamnatin Jihar Zamfara na...

Gwamnatin Zamfara Ta Amshi Tubabbun ’Yan Bindiga Uku

Gwamnatin Zamfara Ta Amshi Tubabbun ’Yan Bindiga Uku

by Sulaiman Ibrahim
16 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Mohammed, Matawallen...

Next Post
Hawa

Korona: An Samu Cinkoson Ababen Hawa A Kano Sakamakon Dokar Takunkumin Fuska

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version