Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Abuja: NAF Na Juyayin Rasa Hazikan Jami’anta Bakwai A Hatsarin Jirgin Yaki

by Muhammad
February 23, 2021
in LABARAI
2 min read
NAF
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Mahdi M. Muhammad,

Rundunar sojin saman Nijeriya (NAF), a safiyar ranar 21 ga Fabrairu 2021, ne ta tabbatar da cewa daya daga cikin jiragen ta, kirar ‘Beechcraft KingAir B350i’ (NAF 201), ya yi hatsari yayin da yake dawowa zuwa filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, bayan da ya bayar da rahoton tsayawar aikin inji a wuraren Minna, inda aka aika shi don gudanar da ayyukan sa-ido a kan jihar Neja da kewaye dangane da kokarin hada karfi don ganin an sako daliban ma’aikatar da aka sace daga Kwalejin Kimiyya ta Gwamnati da ke Kagara, Jihar Neja.

Wannan sanarwar ta fito ne daga hannun Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na rundunar, Air Bice Marshal Ibikunle Daramola, a inda yake cewa, kamar yadda bayani ya gabata, babban hafsan sojin sama (CAS), Air Bice Marshal Oladayo Amao, ya kafa kwamitin bincike domin gano musabbabin hatsarin. Yayin da kwamitin ta fara aikin, NAF, bayan ta sanar da ‘yan uwa da dangin mamatan, da bakin cikin sanar da ma’aikata 7 din da suka rasa rayukansu a hatsarin, wadanda suka hada da;

  1. Flight Lieutenant Haruna Gadzama (Captain).
  2. Flight Lieutenant Henry Piyo (Co-Pilot).
  3. Flying Officer Micheal Okpara (Airborne Tactical Obserbation System (ATOS) Specialist).
  4. Warrant Officer Bassey Etim (ATOS Specialist).
  5. Flight Sergeant Olasunkanmi Olawunmi (ATOS Specialist).
  6. Sergeant Ugochukwu Oluka (ATOS Specialist).
  7. Aircraftman Adewale Johnson (Onboard Technician).

Tun da farko, Shugaban ya ziyarci wurin da hatsarin ya faru, tare da Ministan Tsaro, Manjo Janar Bashir Magashi, Ministan Sufurin Jiragen Sama, Sanata Hadi Sirika, Babban hafsan tsaro, Manjo Janar Lucky Irabor, da sauran shugabannin hafsoshin soji. Shugaban, a madadin hafsoshi, sojojin sama da maza da mata na NAF, yana sake yin ta’aziyya ga dangin mamatan tare da addu’ar Allah madaukakin Sarki ya yi masu rahama kuma yasa sun huta.

SendShareTweetShare
Previous Post

Attahiru Ya Ba Sojojin Kasa Wa’adin Awa 48 Su Kwato Garin Marte

Next Post

Kisan ’Yan Sanda: Kwamishinan ‘Yan Sanda Ya Zargi ‘Yan Kungiyar Asiri

RelatedPosts

Garkuwa

An Kama Sojan Da Ke Kai Wa ‘Yan Ta’adda Kayan Sojoji A Zamfara

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim "An kama wani jami’in soja da budurwarsa...

Aikin Wutar Mambilla  A Takardu Kawai Yake, Inji Gwamnonin Arewa Maso Gabas

Aikin Wutar Mambilla A Takardu Kawai Yake, Inji Gwamnonin Arewa Maso Gabas

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

Kungiyar gwamnonin arewa maso gabas sun nuna rashin jin dadin...

Bindiga

Gwamna Ortom Ya Yabawa Umarnin Buhari Na Hana Mallakar  AK47 Ba Bisa Ka’ida Ba

by Muhammad
6 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Gwamnan Jihar Benue Samuel Ortom a ranar...

Next Post
Kungiyar Asiri

Kisan ’Yan Sanda: Kwamishinan ‘Yan Sanda Ya Zargi ‘Yan Kungiyar Asiri

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version