ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame

byKhalid Idris Doya
9 months ago
Acf

Kungiyar Dattawan Arewa (ACF), ta bukaci sojojin Nijeriya da su sake duba dabarbaru da hikimomin da suke bi wajen magance matsalolin tsaro a arewacin kasar da ma Nijeriya baki daya.

A wata sanarwar da jami’in watsa labarai na kungiyar, Farfesa Tukur Muhammad Baba, ya fitar a ranar Litinin, ACF ta nuna damuwarta kan yadda ake samun ‘yan kura-kurai a aikace-aikacen sojojin.

Kungiyar ta nuna takaici kan yadda jirgin yakin sojoji ya yi luguden wuta a wasu kauyuka biyu a karamar hukumar Silame a Jihar Sakkwato a ranar Laraba, 25 ga watan Disamban 2024.

Harin wanda ya janyo mutuwar fafaren hula goma da jikkata wasu da dama.

Kungiyar Dattawan Arewan ta yaba wa gwamantin tarayya da gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu bisa hanzarin kai dauki da daukan nauyin jinyar wadanda suka raunata tare da bata wani lokaci ba.

“ACF ta kadu sosai da wannan lamarin na Silame, abun ya yi yawa a kasar nan. Irin wannan harin ya faru a kauyen Tudun Biri da ke Jihar Kaduna da Jihar Adamawa da Nasarawa, da jikkata mutane da dama wanda har yanzu muna fama da wadannan radadin a zukatanmu.”

A cewarsa sanarwar, kungiyar a kowani lokaci tana karfafa gwiwar hukumomin tsaro wajen yaki da kowace nauyin ta’addanci a fadin kasar nan, amma ba hakan ba ne zai ba su damar kashe fafaren hula ba tare da sun ji ko sun gani ba.

“Babu wanda ya isa ya shiga shakku game da irin wannan goyon bayan namu, kuma ACF ta yi kira ga duk wani mai kishin kasa a Nijeriya da ya ba jami’an tsaro goyon baya. Abu ne kawai da ba za a yarda da shi ba a bar ‘yan ta’adda da masu aikata laifuka na kowane irin launi su rike al’umma don neman kudin fansa ta hanyar ayyukansu na kiyayya.

“Wannan, abubuwan da suka faru irinsu na Silame da sauran wadanda suka faru kafin shi da kuma kididdigar tasirinsu ga ‘yan kasa marasa laifi suna daukar wani tsari mafi tayar da hankali tare da asarar Dan’adam wanda ba za a yarda da shi ba.”

Daga bisani kungiyar ta yi kira ga sojojin da su maida hankali wajen gudanar da ayyukansu bisa kwarewa da sanin ya kamata domin kauce wa faruwar irin wannan lamarin a nan gaba ta hanyar duba dabarun da hikimomin yaki da suke yi wajen kai farmakisu ga ‘yan ta’adda.

Kungiyar Dattawan Arewan ta kuma nemi masu hannu da shuni da kungiyoyi da su kai agaji da tallafi ga wadanda lamarin ya shafa domin rage musu radadin halin da suke ciki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Next Post
Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version