Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Adadin Jami’an Tsaron Da Ke Kasar Nan, Ba Za Su Iya Kawo Karshen Matsalar Ba- Wanna

by
1 year ago
in RAHOTANNI
2 min read
Jami'an Tsaro
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Muhammad Awwal Umar,

An bayyana cewar kokarin da gwamnatin tarayya ke cewar tana yi dan kawo karshen matsalar tsaro a kasar nan har yanzu da aiki a gabanta, domin matsalolin da ke kasa yafi adadin abinda aka tanada dan magance ta. Alhaji Awaisu Wanna wani jigo mai sharhi akan matsalar tsaro kuma daya daga cikin wadanda suka yi gwagwarmayar dawo da mulki hannun farar hula ne ya bayyana hakan ga LEADERSHIP A YAU.

Idan kana neman yabo ko gwamnatin ta kaunace ka sai ka ce mata tana kokari, amma idan gaskiya ake magana har gobe, zance gwamnati ba ta dauki matakin matsalar tsaro ba a kasar nan, sama da shekaru ake fadawa duniya cewar jami’an tsaron soja da ‘yan sanda da wasu masu kayan sarki da ake anfani da su da sunan tsaro ba su kai adadin kare rayukan ‘yan Nijeriya ba.

Labarai Masu Nasaba

2023: Kotu Ta Yi Fatali Da Karar Emefiele Kan Ministan Shari’a Da INEC

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Gwamnatin tarayya tayi kunnen uwan shegu da wannan abin, a kowani shekara matasa sama da dubu dari ke kammala karatu a kasar nan, kuma ba su da aikin yi kuma ba a nuna masu aikin da zasu yi ba. Idan ma noma ne zasu yi noman ya gagara, duk abinda suke da niyyar yi na dogaro da kai bai yiwu wa dan ba a samar mai ginshiki ba. Tunda shugabancin ma yana kokarin gagarar shugabannin, maganar da muke yi a kullun shi ne yawan adadin jami’an tsaro da samar masu da kayan aiki wadatacce.

ADVERTISEMENT

Tambayar da na ke yi, shi ne ina matsayin rantsuwar da ake yi lokacin karban mulki, wanda yanzu har su masu rantsuwar ba su da tabbas akan yadda abubuwa ke gudana a kasar nan, ba shugaban kasa ba, har kan gwamna akwai inda ba sa iya shiga a kasar nan balle shugaban karamar hukuma, to wani karya za mu yiwa junan mu.

Ya kamata maganar rufe-rufe ta kawo karshe, ya zama dole gwamnati ta canja tunani wajen samar da gurabun ayyuka ga matasan kasar nan, na biyu kuma a tabbatar an baiwa gwamnoni damar taka rawa akan matsalar tsaro, domin babu wata doka a kasar nan da ta ayyana cewar gwamna na da iko koda akan kwamishinan ‘yan sanda ne na jiharsa ba, balle kuma wani kwamandan soja, shi yasa har yau a tarihin kasar nan ba a taba samun rahoton gwamnan da ya bar kujerarsa akan ya kasa kawo karshen matsalar tsaro a jiharsa ba.

A shekarar da ta gabata ‘yan bindigar sun tarwatsa su, sun bar anfani gona wanda da shi suka dogara a rayuwarsu, sun dawo cikin gari kuma ba wani tallafi daga gwamnatin, ka ga duk da cewar zaman da ‘yan bindigar bai dace ba, to amma laifin waye.

Maganar gaskiya akwai bukatar kwalliyar fuska ga yadda ake tafiyar da mulkin kasar nan, ta fuskar daukar aiki da kula da hakkin ma’aikatan.

Idan ka lura, dukkan wadannan matsalolin sun taso ne tun daga kan zabe, domin ‘yan takara ba cancanta ake dubawa ba, jam’iyyun da ake zaba ba nagartansu ake dubawa ba, shi yasa jam’iyyar da tafi karfi, tafi masu kudi a cikinta ita ke kafa gwamnati, su kan su jami’an tsaro da ka ke gani ana anfani da su lokacin zabe babban aikin su kare muradun gwamnati.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Tankin Ruwa Ya Fado Ya Kashe Matashi A Yobe

Next Post

Shugaban Makarantar Fasahar Kiwon Lafiya Na Kano Yana Ayyukan Da Ke Kare Kimar Gwamna Ganduje–Dokta Amina Ganduje.

Labarai Masu Nasaba

2023: Kotu Ta Yi Fatali Da Karar Emefiele Kan Ministan Shari’a Da INEC

2023: Kotu Ta Yi Fatali Da Karar Emefiele Kan Ministan Shari’a Da INEC

by Khalid Idris Doya
2 days ago
0

...

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

by Ahmed Muhammad Dan'asabe
6 days ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

by
6 days ago
0

...

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

by CMG Hausa
6 days ago
0

...

Next Post
Kiwon Lafiya

Shugaban Makarantar Fasahar Kiwon Lafiya Na Kano Yana Ayyukan Da Ke Kare Kimar Gwamna Ganduje--Dokta Amina Ganduje.

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: