Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Addu’ar Bankwana Da Nda-Isaiah Ta Fara Kankama

by Muhammad
December 24, 2020
in MANYAN LABARAI
2 min read
Nda-Isaiah
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
  • Janar Abdulsalami, Etsu Nupe Da Gwamna Sani Sun Jaddada Ta’aziyya

Daga Nasir S. Gwangwazo, Abuja

 

samndaads

Ayyukan gudanar da ayyukan addu’ar bankwana gabanin binne gawar Shugaban kamfanin Rukunin LEADERSHIP, Sam Nda-Isaiah, sun fara kankama a Abuja, babban birnin Tarayyar Nijeriya, a jiya Laraba.

Kamar yadda a ka tsara cewa, za a fara da gudanar da taro ta hanyar bidiyo, don gudanar da addu’o’i a Babban Dakin Taro na Duniya da ke Abuja (ICC), taron ya gudana kamar hakan, inda ya samu halartar shugabannin gudanarwa na LEADERSHIP tare da sauran jiga-jigan kasa.

Idan dai za a iya tunawa, Mista Sam Nda-Isaiah ya kwanta dama ne a ranar Juma’a, 11 ga Disamba, 2020, bayan wata gajeriyar rashin lafiya.

A ranar Lahadin da ta gabata ne, iyalin mamacin su ka fitar da jaddawalin yadda jana’izarsa za ta gudana, a inda suka bayyana cewa, tsofaffi shugabannin Nijeriya, Janar Ibrahim Badamasi Babangida da Janar Abdulsalami Abubakar, za su albarkaci jana’izar marigayin, inda a jiya a ka fara gudanar da ayyukan jana’izar, wacce a ranar ce da a ka gabatar da taro na musamman, don sauraron jawabai daga makusanta da ’yan uwan marigayin.

A cigaba da bikin addi’o’in, a ranar Lahadi mai zuwa a ke sa rai Fadar Shugaban Kasa da ta gwamnatin Jihar Neja (jihar da Marigayi Nda-Isaiah ya fito) za su halarci taron.

Sanarwar, wacce kanin marigayin, Mista Abraham Nda-Isaiah, ya sanya wa hannu, ta kara da cewa, za a gudanar da wakoki na musamman a ranar Lahadin, wato 27 ga Disamba, 2020.

Bugu da kari, Abraham ya ce, “za a gudanar da taron binne marigayin ne a washegari Litinin 28 ga Disamba, 2020, a makabartar Gudu da ke Abuja, Babban Birnin kasar, da misalin karfe 10 na safe, wanda zai zama taro ne na kididdigaggun wadanda a ka gayyata kawai.”

Sam Nda-Isaiah, wanda ya kasance masanin harhada magunguna, dan kasuwa, mashuhuri a harkar yada labarai, kuma hazikin dan siyasa. Mutuwar sa ta girgiza mutane a duk fadin kasar nan da ma kasashen waje.

Duk da ya ke mutum ne wanda ya sami horo a fannin sarrafa magunguna, Sam yana fada da farin ciki cewa, ya dauki aikin jarida a matsayin sana’arsa, kuma ya samu nasarori tun bayan da ya kafa tsayayyar Kamfanin Jaridun LEADERSHIP, ‘National Economy’ da LEDERSHIP A YAU, wacce ta kasance jaridar Hausa ta farko mai fitowa kullum a duniya.

SendShareTweetShare
Previous Post

DSS Ta Fadakar Da ’Yan Nijeriya Shirin Tada Boma-bomai A Wuraren Cunkoso

Next Post

Farfesa Moghalu Ya Yi Wa Gwamnati Gyara Kan Batun Layin Waya Da NIN

RelatedPosts

Bude Makarantu

Korona: Ba Ja Baya Ga Bude Makarantu – Gwamnatin Bauchi

by Muhammad
6 days ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Bauchi ta...

Harshen Hausa

Taron ‘Waiwaye Adon Tafiya’: Masana Sun Damu Bisa Nakasta Harshen Hausa

by Muhammad
1 week ago
0

Akwai Damuwa Kan Yadda Zamani Ke Tafiya Da Al’adun Bahaushe...

'Yan Kwaya

Zaben Kananan Hukumomin Kano: Yadda Aka Tono ’Yan Kwaya A ’Yan Takara

by Muhammad
1 week ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta...

Next Post
Farfesa Moghalu Ya Yi Wa Gwamnati Gyara Kan Batun Layin Waya Da NIN

Farfesa Moghalu Ya Yi Wa Gwamnati Gyara Kan Batun Layin Waya Da NIN

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version