Afrika Ta Kudu Na Neman Hadin Gwiwa Da Sin Wajen Zamanantar Da Kanta
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Afrika Ta Kudu Na Neman Hadin Gwiwa Da Sin Wajen Zamanantar Da Kanta

byCGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Afrika

Babbar jami’ar jam’iyyar ANC mai mulkin Afrika ta kudu, ta ce kasar Sin ta samu gagarumar nasara a kan tafarkinta na zamanantar da kanta, kuma Afrika ta Kudu na ganin akwai dimbin damarmakin hadin gwiwa da Sin wajen inganta zamanantar da kanta. 

 

Gwen Ramokgopa, wadda ita ce babbar ma’ajiya ta jam’iyyar ANC, ta ce dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika (FOCAC), ya cimma kyakkyawan sakamako ta hanyar shirye-shiryen hadin gwiwar moriyar juna.

  • ’Yan Kasuwa Daga Kasashe Da Yankuna 119 Sun Halarci CIFIT Karo Na 24 
  • Dubban Jama’a A Isra’ila Sun Yi Zanga-Zangar Neman Amincewa Da Yarjejeniyar Hamas

Ta ce taron FOCAC, ya kasance wata muhimmiyar dama ta karfafa hadin gwiwar Sin da Afrika a bangarori da dama, musammam a bangaren bunkasa dangantakar tattalin arziki da cinikayya .

 

Taken taron wanda ya gudana daga ranar Laraba zuwa Jumma’a, shi ne “hada hannu domin inganta zamanantarwa da gina al’ummar Sin da Afrika mai makoma ta bai daya bisa babban mataki.”

 

Ta ce idan ana son inganta zamanantar da nahiyar Afrika, akwai bukatar la’akari da albarkar tattalin arzikin nahiyar da yadda za a lalubo damarmakin ci gaba da nahiyar ke da shi, wanda ke nufin kirkiro kyakkyawan muhallin kasuwanci da inganta hidimtawa al’ummar nahiyar da amfana da sabbin fasahohi, ciki har da fasahohi masu tsafta da suka shafi makamashi da motoci masu amfani da lantarki, tana mai cewa, Sin ta kasance jagora a wadannan bangarori, don haka, akwai damarmakin da za a iya karfafa hadin gwiwa da ita don daukaka zamanantar da kasar ta Afrika ta Kudu.

 

Ta kuma yaba sosai da shawarwarin taimakawa nahiyar Afrika bunkasa ayyukan masana’antu da shirin Sin na zamanantar da aikin gona a Afrika da shirin hadin gwiwar Sin da Afrika kan horar da masu basira, wadanda kasar Sin ta gabatar.

 

A cewarta, Sin da Afrika ta Kudu mambobi ne na kungiyar BRICS, kuma wakilan kungiyar kasashe masu tasowa, don haka, hadin gwiwa a tsakanin kasashen biyu a mabambantan dandamali, ya taimaka wajen kara sautin muryar kasashe masu tasowa. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Xi Ya Rattaba Hannu Kan Umarnin Amfani Da Ka’idojin Kare Muhalli A Aikin Soja

Xi Ya Rattaba Hannu Kan Umarnin Amfani Da Ka’idojin Kare Muhalli A Aikin Soja

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version