Aikin Bututun Gas Na Nijeriya - Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aikin Bututun Gas Na Nijeriya – Morocco Na Ƙara Samun Ci Gaba

byAbubakar Sulaiman
3 months ago
Nijeriya

Aikin gina bututun gas tsakanin Nijeriya da Morocco ya kai wani sabon mataki bayan tarukan kwamitin fasaha da na jagoranci da aka gudanar a Rabat, babban birnin Morocco. Wannan gagarumin aiki wanda zai ratsa ƙasashe 13 na Afrika, an tsara shi ne domin isar da iskar gas daga Nijeriya zuwa Turai ta bakin tekun yammacin Afrika, tare da amfanar ƙasashen da bututun zai ratsa.

Sanarwar da Hukumar Harkokin Ma’adanai da Man Fetur ta Morocco (ONHYM) ta fitar ta bayyana cewa an kammala binciken fasaha da na tasirin muhalli a sashin arewa na bututun, yayin da ake ci gaba da irin wannan bincike a sashin kudu daga Nijeriya zuwa Senegal. Har ila yau, an kafa kamfanin da zai jagoranci aikin (Holding Company), tare da ƙirƙirar ƙananan kamfanoni (SPVs) don kula da kowane sashi na aikin.

  • Hukumar CAF Ta Sanar Da Garuruwan Da Za A Buga Gasar AFCON 2025 A Morocco
  • Morocco Za Ta Sake Karbar Bakuncin WAFCON A 2026

A lokacin taron da aka gudanar a Rabat a ranar 10 da 11 ga Yuli, kamfanonin NNPC daga Nijeriya, ONHYM daga Morocco da SOTOGAZ daga Togo sun rattaba hannu kan sabuwar yarjejeniya, wacce ta tabbatar da aikin shiga Togo cikin. Wannan mataki ya kammala haɗin gwuiwa tsakanin dukkan ƙasashen da bututun zai ratsa.

Bututun zai fara daga Nijeriya, ya wuce ta ƙasashen Benin, Togo, Ghana, Côte d’Ivoire, Liberia, Sierra Leone, Guinea, Guinea-Bissau, Gambia, Senegal, da Mauritania kafin ya isa Morocco. Daga nan kuma, zai haɗu da bututun Maghreb-Europe da hanyoyin iskar gas na Turai, tare da samar da gas ga ƙasashen Nijar, Mali da Burkina Faso.

Wannan aikin, wanda aka fara ƙarƙashin jagorancin Sarkin Morocco Mohammed VI da Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, yana da nufin ƙarfafa haɗin kai, tattalin arziƙi, da ci gaban ƙasashen Afrika. Ana sa ran aikin zai zama jigo wajen inganta rayuwar al’ummomi, da haɓaka amfani da makamashi mai tsafta, da ƙarfafa haɗin gwuiwar yankin Atlantic.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Next Post
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Ba Zamu Dawo Da Sanata Natasha Zauren Majalisa Ba, Sai Mun Karɓi Kwafin Hukuncin Kotu - Majalisa

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version