Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Aikin Lantarki Da Kauran Bauchi Ke Yi Wa Yankin Rahama Zai Taimaka – Muktar Kadade

by Muhammad
November 30, 2020
in RIGAR 'YANCI
1 min read
Kauran
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Isah Ahmed

 

samndaads

Wani matashi kuma Sakataren Kungiyar Matasa ta Cigaban Kauyen Kadade da ke Karamar Hukumar Toro a Jihar Bauchi, Muktar Lawal Chikago, ya bayyana cewa, aikin jan wutar lantarki da Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad, ya ke yi a yanzu zuwa kauyukan yankin Rahama zai taimaka wajen bunkasa yankin.

Muktar Lawal Chikago ya bayyana haka ne a lokacin da ya ke zantawa da Wakilin LEADERSHIP A YAU da ke Jihar Filato.

 

Ya ce babu shakka wannan wutar lantarki, da ake son jawo masu, ba karamin cigaba zai kawo wa yankin ba. Don haka matasa da sauran al’ummar wadannan kauyuka, suna godiya da wannan kokari da gwamna yake yi masu.

Ya ce sun yi shekaru da dama, suna neman a jawo masu wannan wuta, amma Allah bai sa sun sami nasara ba, sai a wannan lokaci.

“A wannan yanki mun yi suna wajen ciyar da al’ummar kasar nan. Domin muna noman kayan abinci, kamar masara da shinkafa da waken soya da dawa da rake da tattasai da attaruhu, da ake kaiwa wurare daban daban na kasar nan. Don haka tuni ya kamata ace an samar mana da hanyoyi da wutar lantarki, a wannan yanki.”

Ya yi kira ga al’ummomin wadannan kauyuka, su bada goyon baya da hadin kai, ga wannan aikin jan wuta da ake yi.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnan Ondo Ya Yabi Shirye-Shiryen Rage Radadin Rayuwa Na Gwamnatin Tarayya

Next Post

Fashola Bai Cancanci Zama Ministan Ayyuka Ba – Malam Faruk Danmaje

RelatedPosts

Ingantaccen zabe

Aniyar Ganduje Ce Ta Haifar Da Ingantaccen Zabe A Kano – Yusif Ali

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana cewa, kyakkyawar aniyar Gwamna...

Kaduna

Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Kwanton Bauna A Kaduna

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Sojojin da ke karkashin ‘Operation Thunder...

Farar Hula

Hankula Sun Tashi A Maiduguri Bayan Babbaka Sojan Da Ya Harbi Farar Hula Hudu

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Mutanen Maiduguri sun shiga tararrabi bayan...

Next Post
Fashola

Fashola Bai Cancanci Zama Ministan Ayyuka Ba – Malam Faruk Danmaje

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version