Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

bySulaiman and Leadership Hausa
3 months ago
Malam

A yayin cin zarafin malaman makakarantun Boko da wasu iyayen dalibai da wasu ‘yan uwan daliban Nijeriya ke yi, wanda lamarin ke ci gaba zama ruwan dare, kawai saboda malaman, sun hukunta ‘ya’yan kan wani laifi da suka aikata a makarantun su, domin yaran su zamo na gari, amma lamarin, bai isa ga kafafen yada labarai.

Wannan rashin isar cin zarafin na su ga kafafen yada labaran, ya sanya, malaman da irin wannan lamarin ya rutsa da su, ke ci gaba da jurewa, su kuma yi gum, da bakinsu, ba tare da sun gayawa kowa ba.

Irin wannan cin zarfin, ya faru hatta a kan Mista Aledander Rotifa wanda Mataimakin Shugaban Kwalejin Complete Child Debelopment College ne, da ke a yankin Aule, karamar hukumar Akure ta Arewa North jihar Ondo, a ranar 26 ga watan Mayun 2025, inda aka yi zargin wata uwa madam Dorcas Asije, mahaifiya ga wani dalibi sun yi hayar wasu bata gari sun ci zarfin Aledander.

Dorcas ta aikata wannan ta’asar kan Aledander ne, don kawai ya kwace wayar salular danta a Kwalejin, a yayin don kar ya aikata magudin jarrabawar WASSCE.

Hakan ya sanya Dorcas tare da wani yayanta wanda tsohon dailibi ne a Kwalejin suka je Kwalejin suka yiwa Aledander barazanar aikakata masa ta’asar na ko dai ya kyale danta ya tabka magun jarrabawar da wayar ta sa, da yake zana darasain lissafi.

Kazalika barazanar ta su bata tsaya nan ba, domin a lokacin da Aledander ke a wani ofishin ‘yansanda, nan ma su bishi har can, tare da bata garin da ta yi haya, inda ta mamayi, wata motar ‘yansandan da ke dauke da Aledander, suka fito da shi waje, suka lakada masa na Jaki.

Sai dai, gwamnatin jihar, ta yi hanzarin shiga lcikin lamarin, inda ‘yansanda, suka cafko Dorcas tare da wasu mutane biyar da ake zargi, suna da hannu, wajen aikata ta’asar.

Kazalika, an gurfanar da su a gaban Kuliya, kan tuhumar hada baki, cin zarfi, barazana ga rayuwarsa, tayar da hayaniya a cikin alumma da kuma yunkurin kisan kai.

Amma mai makon wadanda ake zargin, su nuna damuwa kana abinda ake zargin su, tare da kuma gargadin dan nasu, sai kawai majin Dorcas Mista Elisha Imoukhuede, ya buge da rubata takardar korfi, a kan Aledander da kuma a kan ofishin ‘yansanda na gunduma Okuta Elerinla, zuwa ga Babban Sifetan ‘yansanda.

 

Bugu da kari, a ranar 12 ga watan Okutobar 2021, ‘yansanda sun kama wani uba mai suna Abidemi Oluwaseun mai shekara 35, kan zargin kutsawa cikin Kwalejin mata ta Baptist Girls’ College, da ke a yankin Idi-Aba a garin Abeokuta na jihar Ogun da wasu bata gari, da ya yi hayarsu, suka ci zarafin wani malamin makarantar, saboda kawai, ya zane ‘yarsa, mai shekaru 15 da bulala,

Hakazali, a ranar 16 ga watan Nuwambar 2021, wani dalibain jami’ar Ilorin mai suna Salaudeen Waliyullah Aanuoluwa, ya lakadawa malamar da ke koyarwa a jami’ar, mai suna Madam Zakariyyah duka, inda har ta kai ga, ta suma.

Duka cikin watan na Nuwambar 2021, iyayen wata dalibar makarantar Jericho High School da ke a Ibadan, sun yo hayar wasu bata gari, suka lakadawa wasu malaman makarantar duka

Haka a ranar 13 na watan Fabirairun 2025, mahukutan jami’ar Nnamdi Azikiwe da ke a Awka, a jihar Anambra, sun kori wadi dalibi, mai suna Goddy-Mbakwe Chimamaka Precious, bisa cin zarafin wani malamin jami’ar Dakta Chukwudi Okoye, saboda ya dakatar da ita, daga daukar bidiyo ta hanyar kafar TikTok wanda malamin, ya dakatar da ita.

Kazalika, wani malami a wata makarantar kudi a yankin Abrakaa jihar Delta, a ranar 2 na watan Disambar 2021, ya gamu da ajalisan, bayan da ya sha na Jaki, a hannun wani dalibinsa.

Duba da irin wadannan ayyukan na ta’asar, kan malamai, matsayin mu a wannan Jaridar, muna ganin, ga dukkan alamu, batun duk wata kima da malamai ke da ita, ta fara gushewa, musamman duba da yadda a yanzu, girmama na gaba a tsakanin wasu matasa dalibai, ta kau.

Wani karin babban abin takaicin shi ne, yadda wasu iyaye, ke marawa ‘ya’yansu baya, wajen aikata, manyan laifuka, musaman yadda iyayen ke yin uwa da makarbiya, domin ya’yansu, su aikata magun jarrabawa.

Baya ga wannan, wasu iyayen ma, goyawa ‘ya’yansu baya suke yi, domin rungumar damfarar ta yanar Gizo, da aka fi sani da “yahoo”, domin su zamo masu kudi, a dare daya, wanda kuma an sha ruwaito irin wadannan ‘yan Yahoo, har tsafi da rayukan mutane suna yi, bisa nufin neman sa’a.

Ba wai kawai, an kafa makaranta, domin koyar wa bane, ta kuma kasance, waje ne, na koyar da tarbiyya, amma abin bakin ciki, wasu iyayen dalibai, sun kasance suna yin zagon kasa, maimakon su kara karfafa koyar da da’a a tsakanin ‘ya’yansu daliban.

Ko da yake dai, akwai wasu makarantun, da har yanzu, suke ci gaba da yin kokari wajen dakile cin zarafin da wasu daliban, ke yiwa malamansu.

Muna bayar da shawarar cewa, dole ne, a rinka kare rayuwar malamai yayin da suke kan aikinsu na koyar wa.

Kazalika, muna shawartar ‘yansanda, da su tabatar da an gaggauta daukar mataki, kan lamarin da ya auku na Ondo, musamman domin hakan, ya zama izina ga sauran masu tunanin sake aikata haka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fyade
Ra'ayinmu

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Ra'ayinmu

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

August 29, 2025
Ra'ayinmu

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

July 25, 2025
Next Post
Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam’iyyar PDP Ba — Damagum

Ko Kaɗan Bamu Ji Takaicin Ficewar Atiku Daga Jam'iyyar PDP Ba — Damagum

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version