Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTALIN ARZIKI

Akwai Dalilin Kasa Kammala Hanyar Jirgin Kasan Ibadan Zuwa Kano – Amaechi

by Muhammad
January 11, 2021
in TATTALIN ARZIKI
2 min read
Amaechi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Ministan sufuri, Rotimi Amaech ya bayyana cewa, gwamnatin tarayya za ta kammala kwangilar yin titin jirgin kasa tun daga Ibadan har zuwa Kano da zarar gwamnatin kasar China ta bayar da bashin dala 5.3. domin kammala dukkan titin  jiragen kasa ne ya sa gwamnatin Nijeria ta nemo basi daga gwamnatin kasar China. Ministan ya bayyana cewa, sauran masu zuba jari wadanda suke sha’awar taimaka wa Nijeriya wajen ci gaba za su yi hakan daga baya.

Da ake tattaunawa a wani shiri na gidan talabijin  NTA da ke garin Abuja, mahukunta sun bayyana cewa, tuni gwamnatin Nijeriya ta amince da bayar da kwangilar hanyar jirgin kasan.

samndaads

“Muna ciran gwamnatin kasar China ta amince da bayar da bashin dala biliyan 5.3 domin kammala kwangilar titin jirgin kasa tun daga Ibadan har zuwa Kano. Gwamnatin tarayya ta bayar da kwangilar tun a shekarar da ta gabata.

“A duk  lokacin da gwamnatin tarayya ta samu nasarar samun bashin dala biliyan 5.3 daga gwamnatin kasar China, to za a kammala kwangilar titin jirgin daga Ibadan zuwa Kano.

Mista Amaechi ya bayyana cewa, titin jirgi tsakanin Ibadan zuwa Kano zai hade yankuna guda shiga wadanda suka hada da Kaduna zuwa Kano da Abuja da Minna da Ilorin da Oshogbo da Ibadan, inda za a dunga kai kayan jirgi tun daga Legas zuwa Kano.

Ya kara da cewa, idan aka samu nasarar kammala aikin, za a samu raguwar hadararruka, sannan za a dunga kai kayayyakin a jirgin kasa tun daga Legas har zuwa Ibadan.

Ya ce, idan aka samu nasarar kammala titin jirgin kasa daga Ibadan zuwa Kano, to za a dunga safarar kayayyaki tun daga Legas har zuwa Kano ta jirgin kasa ba tare da wata matsala ba.

Ya ci gaba da cewa, ya kamata ‘yan Nijeriya su kara hakuri an kusa share musu hawayansu a bangaren sufuri ta jiragen kasa. Misa Amaechi ya ci gaba da cewa, ma’aikatan kude ce take bayar da kudaden ayyukan jiragen kasa ba ma’aikatan sufuri ba. Ya kara da cewa, shugaban kasa ya amince da amso bashin kudaden domin a samu nasarar gudanar da ayyukan yadda ya kamata.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kwari Sun Mamaye Gonakin Manoman Tumatir A Jos

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa NERC Umarnin Dakatar Da Karin Kudin Lantarki

RelatedPosts

Kasafin 2021

Buhari Zai Kaddamar Da Cibiyar Mai Da Gas Ta Kasa A Legas

by Sulaiman Ibrahim
20 hours ago
0

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kaddamar da cibiyar mai da...

An Nemi Matakan Gwamnati Su Rage Yawan Mukaman Siyasa Don Zuba Jari A Noma

Bai Kamata A Fake Da Tallafi A Azabtar Da ’Yan Nijeriya Ba, Inji NLC

by Sulaiman Ibrahim
20 hours ago
0

kungiyar kwadagon Nijeriya (NLC) ta bayyana cewa, bai kamata gwamnatin...

Kasafin 2021: Buhari Da Osinbajo Za Su Ci Abinci Da Balaguron Naira Biliyan N3.4

Kasafin 2021: Buhari Da Osinbajo Za Su Ci Abinci Da Balaguron Naira Biliyan N3.4

by Sulaiman Ibrahim
20 hours ago
0

Shugaban kasa Muhammadu Buhari da mataimakinsa Yemi Osinbajo za su...

Next Post
NERC

Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa NERC Umarnin Dakatar Da Karin Kudin Lantarki

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version