Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Akwai Gidajen Biredi 7,400 Masu Rajista A Kano — Kungiyar Masu Biredi

by Tayo Adelaja
September 17, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Ibrahim Muhammad da Mustapha Ibrahim Tela, Kano

Kungiyar masu gidajen Biredi ta kasa reshen Jihar Kano, karkashin shugabancin sabon shugabanta, Alhaji Mu’azu, wanda aka fi sani da Alhaji Mu’azu Gidauniya Bread ta bayyana cewa taana da gidanjen biredi da ta yi wa rijista sun kai 7,400 a Kano kawai, wanda suke da matasa da suka dauka aiki sama da dubu 100, wanda suke aiki a sako da lungu na jihar Kano.

samndaads

Wannan bayani ya fito ne daga bakin mai ba kungiyar shawara ta fuskar shari’a, Alhaji Danladi Baba Kwanar Dawaki, wanda kuma shi ke da ‘Bilkisu Bread’ a lokacin da yake bayani a lokacin rantsar da shugaban kungiyar da sauran shugabanni a kungiyar a dakin taro na Central Hotel Kano, inda ya ce yanzu za su yi amfani da damar su wajen kawar da bata gari a wannan kungiya.

Kamal Muhammd Abubakar mai lakabin ‘Zamani Bread’ shi ne Babban Jami`i a kungiyar da ya Jagoranci gabatar da zaben, ya ce sun yi zabe cikin Nasara idan aka yi la`akari da wadanda aka zaba, kamar irin su Alhaji Alhasan Danhasan, shugaban Amintattu na kungiyar, wanda ya yi alwashin kawo sauyi mai ma`ana, musamman na su ga an rage tashin gwauron zabi na kayayyakin da ake hada biredi

A wata zantawa da ya yi da wakilanmu, Shugaban dattawan kungiyar ta masu gidajen Borodi, Alhaji Aminu Alhasan Danhasan ya bayyana cewa masu yin biredi a Kano, suna samar da aikin yi ga dimbin mutane, domin a cewarsa, in banda gwamnati ba wasu masu sana,a da suke bada aiki ga jama’a kamar kungiyar tasu.

Ya kara da cewa kungiyar tasu ta gudanar da zaben nana ne domin ci gaba da inganta harkokinta. Inda ya tabbatar da cewa Biredin da suke yi ya fi duk irin biredin da sabbin kamfanonin zamani ke yi a dadin dandano da inganci, sai dai kawai a nuna masu kyalkyali.

SendShareTweetShare
Previous Post

“Gwamnati Ta Bar Zaizayewar Kasa Na Haifar Da ’Yan Gudun Hijira A Gombe”

Next Post

Kungiyar ANGO Ta Yi Tir Da Karkatar Da Kayayyakin ’Yan Gudun Hijira

RelatedPosts

Gina Hanyar Ruwa: Babu Kudin Kowa A Cikin Wannan Babban Aiki, Inji Mai Turaka

Gina Hanyar Ruwa: Babu Kudin Kowa A Cikin Wannan Babban Aiki, Inji Mai Turaka

by Daurawa Daurawa
5 hours ago
0

Mai taimakawa gwamna Masari akan wayar da kan jama’a akan...

’Yan Sandan Kano Sun Cafke Mace Mai Garkuwa Da Mutane

’Yan Sandan Kano Sun Cafke Mace Mai Garkuwa Da Mutane

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ta shaida cewar wata mace...

Ta’aziyar Rasuwar Sam Nda Isaiah

Sam Nda-Isaiah Ya Rasu Lokacin Da Ake Tsananin Bukatar Gudunmawarsa – Jami’ar Jos

by Sulaiman Ibrahim
4 days ago
0

Shugabannin jami’ar Jos sun bayyana rashin jin dadinsu dangane da...

Next Post

Kungiyar ANGO Ta Yi Tir Da Karkatar Da Kayayyakin ’Yan Gudun Hijira

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version