Akwai Hannun Gwamnan Kano Wajen Fitar Da Murja Kunya Daga Gidan Gyaran Hali - Jaafar Jaafar
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Hannun Gwamnan Kano Wajen Fitar Da Murja Kunya Daga Gidan Gyaran Hali – Jaafar Jaafar

byLeadership Hausa
2 years ago
Kano

Babban Editan jaridar yanar gizo ta Daily Nigerian,Jaafar Jaafar ya bayyana cewa, “Tun da gwamna bai ba wa na kusa da shi dama ko fuska su ba shi shawara ba, to kuwa lallai haƙƙi ya rataya a kan duk mai kishin Kano ya faɗa masa gaskiya. “

“Mai girma Gwaman Kano, Abba K. Yusuf, sai ka gyara mu’amillarka da mashawartanka da kuma masu riƙe da muƙaman gwamnati.”

  • Sheikh Daurawa Ya Sauka Daga Muƙaminsa Na Shugaban Hisbah Kano
  • Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

“Zancen da mu ke ji shi ne kwamishina sai ya yi wata da watanni ya na son ganin gwamna kan abu mai muhimmanci amma ya kasa gani ko magana da gwamna ta waya. Wannan bai kamata ba, domin kuwa hannu ɗaya ba ya ɗaukar jinka.”

“Binkicen da na yi ya nuna cewa Mallam Daurawa ya yi yunƙurin ganin gwamna don tattauna da shi kan matsalar Murja Kunya amma gwamna bai ba shi dama ba. Ya yi yunƙurin yi masa bayani ta waya, nan ma abin ya ci tura.”

“Sukar da gwamna ya yi wa Hukumar Hisba jiya a bainar jama’a kamar mutum ne ya daɓa wa kansa wuka, domin kuwa gwamnatinsa ya zaga. Kuma dole jama’a su ce saboda Hisba ta kama Murja Kunya gwamna ya yi wannan magana, domin kuwa a lokacin da Hisba ta ke kama masu baɗala ta na jefa su a bayan mota gwamna bai ce uffan ba sai bayan an kama wannan yarinya.”

“Duk mai hankali ya san cewa akwai hannun gwamna (ba wani gwamnati, GWAMNA) dumu-dumu a fitar da murja daga gidan yari ba bisa doron doka ba.”

“ ‘Yan watannin baya kamar mu haukace saboda ana yunƙurin kawar da gwamnatinka ba bisa doron doka ba, amma abin takaici kai kuma ka yi wa doka hawan ƙawara saboda wata ballagaza bankaura.” Cewar dan jarida Jaafar Jaafar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Next Post
Pogba Zai Ɗaukaka Ƙara A Kan Dakatar Da Shi Daga Buga Ƙwallo Na Tsawon Shekaru 4

Pogba Zai Ɗaukaka Ƙara A Kan Dakatar Da Shi Daga Buga Ƙwallo Na Tsawon Shekaru 4

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version