Al-Hilal Ta Kafa Tarihin Lashe Wasanni 28 A Jere
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al-Hilal Ta Kafa Tarihin Lashe Wasanni 28 A Jere

byAbba Ibrahim Wada
2 years ago
Al-Hilal

Kungiyar kwallon kafa ta Al-Hilal dake Saudi Arabiya, ta zama ta farko da ta kafa tarihin cin wasa da yawa a jere, bayan da ta doke Al-Ittihad 2-0 a gasar cin kofin Champions League na Asia.

Wasa na 28 a jere kenan da kungiyar ta yi nasara jimilla da ba mai wannan tarihin a duniya kuma wadda ke rike da bajintar a baya ita ce wata kungiya a Wales, The New Saints a 2016 wadda ta yi nasarar cin wasa 27 a jere.

  • Ana Amfani Da Na’urar Hakar Mai Ta Zamani Da Kamfanin Sin Ya Kera A Uganda
  • Uwargidan Shugaban Kasa Ta Bude Makaranta Ga Matan Da Aka Kora A  Manyan Makarantu A Bauchi

Al-Hilal, wadda take da fitattun ‘yan wasa ciki har da tsohon dan wasan Fulham, Aleksandar Mitrobic ta ci wasa 28 a jere tun daga 1-1 da Damac ranar 21 ga watan Satumba.

Shima tsohon dan wasan Wolbes, Ruben Nebes na buga wa Al-Hilal wasa har da dan kwallon Brazil, Neymar, wanda ya koma kungiyar daga Paris St-Germain kan kudi fam miliyan 77.6 har da tsarabe-tsarabe.

Koda yake Neymar na jinya tun raunin da ya ji a cikin watan Oktoba kuma har yanzu bai warke ba duk da cewa a kwanakin baya an fara rade radin cewa kungiyar za ta soke kwangilar da suka kulla da dan wasan.

Al-Hilal, wadda tsohon kociyan Benfica da Flamengo, Jorge Jesus ke jan ragama tana ta dayan teburi a babbar gasar Saudi Arabiya ta bana, sannan ta kuma bai wa kungiyar da Cristiano Ronaldo ke buga wasa wato Al-Nassr tazarar maki 12.

Dan wasa Mitrobic ya ci kwallo 26 daga 81 da Al-Hilal ta zura a raga a wasa 28 da ta yi nasara a jere kuma ta lashe wasa 16 a lik da uku a wasannin cikin gida da kuma tara a Champions League na Asia.

Nasarar da Al-Hilal ta yi ranar Talata ya sa ta ci kwallo 4-0 gida da waje ta kuma kai dab da karshe a gasar zakarun Turai ta Asia ya yin da tuni aka doke kungiyar Al-Nassr da Cristiano Ronaldo yake bugawa wasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar
Wasanni

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Next Post
Sin: Bai Kamata ‘Yancin Fadin Albarkacin Baki Ya Zama Kafar Nuna Kiyyaya Ga Musulmai Ba

Sin: Bai Kamata ‘Yancin Fadin Albarkacin Baki Ya Zama Kafar Nuna Kiyyaya Ga Musulmai Ba

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version