Alamar Deepseek" Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya

byCGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
DeepSeek

An wallafa wata makala a shafin yanar gizo na gidan rediyon muryar Nijeriya (Voice of Nigeria) a jiya Litinin, inda aka ce, yadda kamfanonin Sin suka samar da manhajojin kwaikwayon tunanin dan Adam (AI) na “open source” (masu barin kofar gyara da ba da damar gyara tsare-tsarensu don biyan mabambantan bukatu), ya nuna yunkurin Sin na sa kaimi ga sabuntawar fasahar AI, da samar da karin damammakin hadin gwiwa da bangarorin duniya.

Hakika dimbin kafofin watsa labaru na duniya sun sa lura kan yanayin “open source” na manhajojin AI na Sin. Misali, shafin yanar gizo na Techish na kasar Kenya ya ce, manhajar DeepSeek ta Sin za ta samar da taimako ga kwararru masu tsara manhaja na kasashen Afirka, domin su kirkiro manhajojin da za su biya bukata wajen magance dimbin kalubalen dake fuskantar kasashensu.

  • Kantoman Ribas Ya Naɗa Farfesa A Matsayin Sakataren Gwamnati
  • Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi

Sai dai, me ya sa aka mai da manhanjojin AI na Sin na “open source”? Dalili shi ne, wannan nau’in manhaja dake iya biyan bukatun karin jama’a na samun karbuwa sosai a kasashe daban daban. Kana yadda karin mutane na kasashen suka fara amfani da manhajar, zai sa a dinga inganta fasahohin da ta kunsa a kai a kai.

Ma’anar aiwatar da matakin “open source” kan manhajojin AI ita ce, maye gurbin tsohon tunani na babakere da son kai, da sabon tunani na tabbatar da bude kofa, da daidaito, da amfanin kowa, da samun ci gaba a kai a kai. Idan mun lakabta wa matakin maye gurbi nan “alamar DeepSeek”, to, za mu iya ganin alamar a manyan harkokin duniya.

A kwanan baya, James Vance, mataimakin shugaban kasar Amurka ya yi jawabi a wajen wani biki cewa, dalilin da ya sa kasashen yamma kirkiro manufar dunkulewar duniya, shi ne domin neman ba kasashe masu sukuni damar samar da kayayyaki masu daraja, wadanda ke kunshe da fasahohin zamani, kana a sanya kasashe marasa karfin tattalin arziki cikin kulawa da ayyukan samar da kayayyaki masu rahusa, wadanda tsarinsu ba shi da sarkakiya. Maganarsa ta nuna niyyar kasashen yamma ta kare tsarin duniya da suka shata, wanda ya kayyade matsayin kasashe marasa karfin tattalin arziki a bangaren samun kudin shiga kadan-kadan, da bin umarnin kasashe masu sukuni.

Sai dai, tabbas za a karya tsarin, ganin yadda ba a samun adalci a ciki. Mun san kasar Sin daya ce daga cikin kasashen da suka warware dabaibayin hana ci gaba da kasashen yamma suka daura musu, inda ta raya tattalin arzikinta, tare da taka muhimmiyar rawa a cikin tsarin duniya ta fuskar samar da kayayyaki.

Daga bisani me kasar Sin ta yi? Ta samar da tunanin gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya, inda aka nanata bukatar ba sauran mutane damar jin dadin zaman rayuwa, matukar wani mahaluki na son samun zaman rayuwa mai inganci. Bisa wannan tunani ne, kasar Sin ta samar da jerin shawarwari masu alaka da ci gaban tattalin arziki, da tsaro, da cudanyar mabambantan al’adu a duniya, da tsayawa kan manufofin tattaunawa tare, da gudanar da aikin gini tare, da raba moriya, gami da sanya kowa a turbar samun biyan bukata, ta yadda kasar ke ta samun amincewa da goyon baya daga karin kasashe.

Tunanin al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makomar bai-daya, da manhajojin AI na “open source”, duk sabbin dabarun daidaita al’amura ne. A lokacin da wani tsohon abu ya gaza biyan bukata, ya kamata a gwada wani na sabo. Ko ba haka ba?(Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

September 30, 2025
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

September 29, 2025
Next Post
majalisar kasa

Nijeriyar Jiya Da Yau: Kiki-Kakar Sabgar 'Yan Majalisu

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version