Alhaji Amadu Umar Ya Zama Sarkin Hausawan Garin Agbara A Jihar Ogun
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alhaji Amadu Umar Ya Zama Sarkin Hausawan Garin Agbara A Jihar Ogun

byBala Kukuru
9 months ago
Alhaji

A makon da ta gabata ne, Majalisar Sarakunan Yarabawan Unguwar Awori Igbasa da ke yankin Agbara karkashin Mai Martaba Sarkin Yarabawa, Oba Mohomod Saeed Idioke na Jihar Ogun ta nuna amincewarta tare da ba da izinin nada Alhaji Amadu Umar, a matsayin Sarkin Hausawan garin Agbara da kewayenta.

Taron nadin sarautar ya samu halartar wadansu daga cikin sarakunan Yarabawa da na Hausawan mazauna Jihar Ogun da Legas da sauran al’umma baki daya. Taron ya gudana ne a harabar fadar Mai Martaba Sarkin Yarabawan yankin na Idioke da ke garin Agbara.

  • Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Legas Za Ta Kara Samar Da Kwararru – Kwamishina
  • Dalilin Da Ya Sa Legas, Abuja, Kaduna Suka Samu Masu Zuba Hannun Jari A Zango Na Uku

Alhaji Amadu ya kasance dan asalin Jihar Jigawa mazaunin Jihar Ogun, inda Sarkin Yarabawan ya ummurci sakataren fadarsa tare da ba shi izinin karanto kyawawan halayen Sarkin Hausawan da kuma bayyana dalilan da suka sa Majalisar Sarakunan Yarabawan ta ba shi wannan sarauta.

Sakataren fadar sarkin Yarabawa ya ci gaba da bayyana cewa Majalisar Sarakunan Yarabawan ta amince da nadin Alhaji Amadu a matsayin Sarkin Hausawan garin Agbara bisa kyawawan halayensa da kuma kokarinsa na hada kan Hausawa da sauran kabilun Yarabawa mazauna yankin, domin su ci gaba da samun zaman lafiya a tsakaninsu baki daya.

Ya ce sun kwashe shekaru da dama suna cudanya da shi ta fuskar zaman lafiya da sauran al’amuran rayuwa na yau da kullum. Bugu da kari, sakataren sarkin Yarawan ya ci gaba da cewa tun daga lokacin da suka san juna da Alhaji Amadu zuwa yanzu ba a taba samun shi yana rigima da wani ba.

Sabon Sarkin Hausawan na garin Agbara a Jihar Ogun, Alhaji Amadu ya yi jawabin godiya ga Majalisar Sarakunan Yarabawan unguwar Awori Igbasa da ke yankin Agbara dangane da cancantar da suka ga ya yi suka ba shi wannan sarauta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Durƙushewar Masana’antu: An Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo  Ƙarshen Matsalar Wutar Lantarki

Durƙushewar Masana’antu: An Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo  Ƙarshen Matsalar Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version