Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Alhazan Jihar Bauchi Sun Fara Dawowa

by Tayo Adelaja
September 27, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya, Bauchi

A karon farko, jirgin alhazan Jihar Bauchi ya fara dawowa daga kasa mai tsarki dauke da alhazan Jihar Bauchi kimanin su 295, daga cikin adadin na alhazan mutum hudu daga cikin ma’aikatan hukumar jin dadin alhazai ne a yayin da sauran adadin kuma dukkaninsu alhazan Jihar Bauchi ne.

Kamfanin jigilar alhazai na ‘Flynas’ ne ya kawo alhazan daga Jidda inda suka iso Bauchi da misalin karfe 4:45 na yamma. Alhazan sun fara dawowa ne a jiya Talata bayan da suka yi nasarar gabatar da ibadunsu na aikin hajji a cikin wannan shekarar na 2017. Ana sa ran alhazan Jihar Bauchi za su ci gaba da dawowa gida ba tare da samun tangarda ba.

A wani labarin kuma, kimanin alhazan Jihar Bauchi su uku 3 ne suka riga mu gidan gaskiya a yayin da suke kan aiyukan ibadarsu na aikin hajji a wannan shekarar 2017. Alhazai biyu daga karamar hukumar Shira wadanda suka rasu a kwanakin baya a sakamakon rashin lafiya, a yayin da wani alhajin shi kuma ya rasu a ranar lahadin nan da ta gabata a sakamakon ciwon zuciya.

Da yake tabbatar da rasuwar na Alhazan jami’in lafiya na hukumar jin dadin alhazan jihar Bauchi Muhammad Dan Azumi Haladu ya ce alhazai biyu da suka rasu dukkaninsu sun fito ne daga karamar hukumar shira a yayin da kuma wani alhazan ya sake rasuwa a ranar lahadin da ta gabata “Shi wannan alhazan jihar Bauchi ne amma ya biya ne daga ofishin hukumar alhazai, alhazan wanda ciwon zuciya ya kashe san, zai iya kaiwa shekaru 55. Ya rasu ne a sakamakon ciwon day a damesa nina kaisa asibiti ana kokarin duba lafiyarsa daga baya rai yayi halinsa”. In ji sa

Jami’in lafiyar ya shaida cewar ya zuwa yanzu dai alhazan jihar Bauchi suna ci gaba da samun kulawa sosai ta fuskacin kula da lafiyarsu da kuma kiwon lafiyarsu ya bada tabbacin cewar shirye shiryen dawow da alhazan jihar Bauchi gabaki dayansu ma ya yi nisa.

Mamba a kwamitin jin dadin alhazan jihar Bauchi Shaikh Isma’il Bajoga ya shaida cewar dawowar alhazan jihar Bauchi ne yanzu suka nufa suke kuma kai, ya bayyana cewar alhazan jihar Bauchin za su dawo ne a jere “Dukkan tsarin da aka yi suna jere kuma suna tafiya daidai, insha Allahu alhazan jihar Bauchi za su ci gaba da dawowa ne a jere. Babu jinkiri, ana kan diban kayan alhazai ma”. In ji shi

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamna Yari Ya Kalubalanci Jami’an Tsaro Sace Mutane Ke Tsorata Masu Zuba Hannun Jari -Dangote

Next Post

Gidan Rediyon Katsina Zai Fara Shirin Taimakon Kungiyoyi

RelatedPosts

‘Yan Ta’adda Sun Kona Ofishin ‘Yan Sanda A Inugu

‘Yan Ta’adda Sun Kona Ofishin ‘Yan Sanda A Inugu

by Sulaiman Ibrahim
3 mins ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Hankula sun kara tashi a wasu yankuna...

Dabbobi

Zamanin Kiwon Dabbobi A Sake Ya Shude – ACF

by Muhammad
7 hours ago
0

Kungiyar Ta Goyi Bayan Matsayin Gwamnonin Arewa Daga Abubakar Abba,...

Garkuwa

Neja Ce Kan Gaba Wajen Fuskantar Matsalar Masu Garkuwa Da Jama’a- Gwamna Bello  

by Muhammad
7 hours ago
0

Daga Muhammad Awwal Umar, Gwamnan Neja, Abubakar Sani Bello ya...

Next Post

Gidan Rediyon Katsina Zai Fara Shirin Taimakon Kungiyoyi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version