Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home Uncategorized

Al’ummar Gundumar Basawa Sun Karrama Dan Majalisarsu

by Tayo Adelaja
September 26, 2017
in Uncategorized
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Sabo Ahmad, Bello Hamza.

 A makon da ya gabata ne al’ummar garin Migoma tare da hadin gwiwar kungiyar yada manufar dan majalisa dokokin jihar Kaduna mai wakiltar gundumar Basawa da ke karamar hukumar Sabon-garin, Zariya, Muktar Isa Hazo, suka karrama shi da lambar yabo bisa ayyukan da ya kawo wa gundumar na raya kasa da ci gaban al’umma.

A jawabin da ya gabatar wajen bikin karramawar, shugaban kungiyar ta yada manufar danmajalisar Hamza Idris Jika, ya bayyana cewa, dalilin da ya sa suka karrama shi, shi ne, su da yake ’yangida ne sun san waye danmajalisar, saboda haka ko lokacin da ya fito takara sun kasance tare da shi, kuma sun ji irin alkawuran da ya dauka lokacin yakin neman zabe, babban a bin da ya karfafa musu gwiwa na karramawar shi ne, yadda ya sauke da yawa daga cikin alkawuran da ya dauka, musamman aikin hanyar da tashi daga Milgoma zuwa Kwakwaren-manu, wanda aiki ne da al’ummar wannan yanki suka yi shekaru suna bukatar a yi musu, amma hakan ba ta samu ba, sai a wannan lokaci. Sannan kamar yadda ya ce, danmajalisar ya tallafa wa matasa wajen karo ilimi da koyon sana’o’i da sauran wadansu fannuka a rayuwa don samun ci gaba.”Saboda haka, muka ya dace mu nuna yabawarmu ga danmajalisar bisa wannan tagomashi da yake yi mana  a wannan yanki, shi ne ya sa muke karrama shi a wannan guri a halin yanzu, wanda kuma nan ce mahaifarsa”.

Shi kuwa a nasa jawabin danmajalisar, ya nuna godiyar ga wadanda suka karrama shin, sannan ya ce, wannan karrama ta kara masa karfin gwiwar ci gaba da gudanar da ayyukan alheri ga al’ummarsa, sannan kuma ta kara fito masa da kyakkyawar dangantakar da yake da ita da a’ummarsa. Wannan ma ta sa danmajalisar yake cewa, dukkan wanda yake ikikrarin ba a maimaita mulki to rashin irin wannan dangantaka ce tsakanin sa al’ummarsa. “Ina alfaharin cewa, kullum ina tare da mutanena, ba na guje musu,ina kokarin biya musu bukatu daidai gwargwado, saboda haka maganar maimaita wa ba na haufi, da yardar Allah za mu kasance a kundin tarihi da za mu karya wanna tsinuwa. Domin ni a gurina tsinuwa ce ke sa a kasa maimaita wa.

Taron ya samu halartar sarakuna da masu unguwannin yankin da sauran al’ummar da ke fadi wannan mazaba.

SendShareTweetShare
Previous Post

Jihohi Uku Ne Suka Yi Bukin Sabuwar Shekarar Musulunci

Next Post

Hukumar NDLEA Ta Nemi Hadin Kan Al’umma A Kano

RelatedPosts

BIDIYO: Manyan ‘Yan Kasuwar Kano Sun Jinjinawa Dangote Kan Rashin Ƙara Farashi

BIDIYO: Manyan ‘Yan Kasuwar Kano Sun Jinjinawa Dangote Kan Rashin Ƙara Farashi

by Daurawa Daurawa
21 hours ago
0

A cikin wannan hira za a ji yadda manyan 'yan...

Tsaro

Ramadan: Gwamnan Gombe Ya Yi Kira Ga Musulmi Su Himmatu Da Addu’o’i Kan Rashin Tsaro

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Khalid Idris Doya, A yayin da al'ummar Musulman duniya...

Gwamnatin Kaduna Ta Yi Wa Karnuka 6,250 Allurar Rigakafin Cutar Rabis

Gwamnatin Kaduna Ta Yi Wa Karnuka 6,250 Allurar Rigakafin Cutar Rabis

by Sulaiman Ibrahim
6 days ago
0

Daga Bello Hamza, Abuja Gwamnatin jihar Kaduna ta samu nasarra...

Next Post

Hukumar NDLEA Ta Nemi Hadin Kan Al’umma A Kano

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version