Amaechi Ga ‘Yan Nijeriya: Akwai Dan Siyasar Da Ya Taba Ce Muku Shi Ba Barawo Ba Ne?
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amaechi Ga ‘Yan Nijeriya: Akwai Dan Siyasar Da Ya Taba Ce Muku Shi Ba Barawo Ba Ne?

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Amaechi

Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya zargi ‘yan Nijeriya da yin tsayuwar daka wajen amsar dukkanin wani abin da aka bijiro musu da shi walau mai kyau ko akasin hakan.

Ya nuna cewa wasu abubuwan sun bayyana wa ‘yan Nijeriya a zahirance, amma kuma suna ci gaba da rungumar abubuwa yadda suka zo a maimakon yin abin da ya dace.

  • Tun Ina Yarinya Ba Na So Na Ga Ana Zaman Banza -Rukayya Usman
  • CMG Da IOC Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

Amaechi, wanda ya shiga harkokin siyasa a 1999 zuwa 2023, wanda ke magana a matsayin babban bako a taron lakca na shekara-shekara na TheNiche wanda ya gudana a cibiyar NIIA da ke Victoria Island a jihar Legas ranar Alhamis.

Duk da cewa an riga an bada rahoton abubuwan da suka wakana a wajen taron, sai dai a halin yanzu wani bidiyo mai tsawon mintina hudu na ci gaba da karade yanar gizo da ke kara daukar hankali.

A bidiyon, tsohon kakakin jihar Ribas kuma gwamnan jihar har sau biyu, ya bayar da dalilan da suka sanya ya yi gum da bakinsa, daga cikin dalilan har da cewa hadiminsa a bangaren yada labarai ya shawarcesa da ya yi shiru.

“Akwai gidajen talabijin da daidaikun da suka yi ta samu na da cewa na yi magana kan batutuwa daban-daban tun lokacin da na bar ofis, amma na ki amincewa na yi maganar. Na ki yin hakan ne bisa dalilai guda biyu, na daya hadimina a bangaren yada labarai ya shawarce ni da kada na ce komai, ya fusata sosai da nake magana da ku.

“Na biyu, ‘yan Nijeriya ba su mayar da hankali kan komai ba. Abu saboda kawai da za a ce, ‘yan Nijeriya ba su kula kan komai, suna rungumar komai yadda ya zo musu. Akwai wani dan siyasa da ya taba ce muku shi ba barawo ba ne? wani dan siyasa ne ya halarci jami’a? wacce ‘yar siyasa ce ta ce muku ta yi hidimar kasa NYSC, sannan wani dan siyasa ne ya gaya muku yana da satifiket?”

Ya kara da nuni da cewa, duk da ‘yan Nijeriya sun san wasu ‘yan siyasar da ba su dace ba, amma har yanzu suna ci gaba da ba su dama.

“’Yan Nijeriya sun sani amma har yanzu suna ci gaba da zabarsu, don haka menene matsayarku? Don me ma zan yi magana alhali ba wani abu ne sabo ba? ‘yan Nijeriya su ne ke da damar zabin wanda suka aminta da wanda ba su gamsu da ba, ‘yan Nijeriya ke zaban wadanda za su zaba da wadanda ba za su zaba ba. Kai, koda ka je gidan dan Nijeriya ka kashe mahaifiyarsa, babbansa zai ci gaba da harkokin rayuwarsa. Babu wani abun da zai dameka, babu fa, don haka menene zai sa na tsaya bata lokacina?”

Tsohon ministan ya ce tun lokacin gwamnatin Jonathan zuwa ta Buhari an yi ta tafka muhawara da zuba maganganu sosai amma duk da haka jiya-i-yau don haka ne ya zabi ya zauna cikin gida ya ja bakinsa ya yi shiru kawai.

Ministan ya kara da cewa ‘yan Nijeriya ba su son gaskiya, har ma ya buga misali da cewa koda mutum ya fito ya ce musu shi karya yake musu ko kuma ya tafka wani laifin amma za su cigaba da amincewa da shi koda kuwa ya ma je gidan yari ya fito.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Jaddada Muhimmancin Samar Da Kyakkyawar Fahimtar Al’ummantaka Ga Jama’ar Kasar Sin

Xi Jinping Ya Jaddada Muhimmancin Samar Da Kyakkyawar Fahimtar Al'ummantaka Ga Jama’ar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version